Shugaban Jam’iyar APC Na Jihar Ekiti Ya Mutu

Shugaban jam’iyar APC na jihar Ekiti, Paul Omotoso ya mutu .

Wata majiya dake kusa da iyalinsa ta ce Omotoso ya mutu ne da tsakar daren ranar Laraba bayan gajeriyar rashin lafiya.

An bada rahoton cewa ya halarci wani taron siyasa ranar Litinin inda aka garzaya da shi asibiti a Ado-Ekiti a ranar Talata bayan da yayi ƙorafin cewa yana jin zazzaɓi. Ya mutu a asibitin Ado-Ekiti.

A wata sanarwa tsohon gwamnan jihar, Kayode Fayemi ya bayyana Omotoso a matsayin ” Shugaba mai sadaukar da kai, mai hada kan mutane kuma jigon jam’iyar APC a jihar.”

Fayemi ya ce ” Mutuwar shugaban jam’iyar rana tsaka ta bar giÉ“i da za a wahala  kafin a cike shi.”

More News

Gwamnatin Adamawa Ta Ƙara Hutun Ɗaliban Makarantu Saboda Annobar Cutar Ƙyanda

Gwamnatin jihar Adamawa ta tsawaita lokacin komawar É—aliban jihar makarantunsu domin fara  zangon karatu na uku saboda annobar cutar Æ™yanda. A wata sanarwa ranar Litinin,...

Sojan Jamhuriyar Nijar sun kama Gawurtaccen ÆŠan Fashin dajin Najeriya Kachalla Mai Daji

Dakarun sojan Jamhuriyar Nijar sun samu nasara kama gawurtaccen É—an fashin dajin nan mai suna Kachalla Mai Daji a garin Illela dake kan iyakar...

Ƴan Fashin Daji Sun Kashe Mutane 7 A Jihar Kebbi

Mutane 7 aka bada rahoton ƴan fashin daji sun kashe  a garin Tudun Bici dake ƙaramar hukumar Danko Wasagu ta jihar Kebbi. A cewar mazauna...

Tsoffin gwamnoni sun wawashe sama da naira tiriliyan 2 tun komawa dimokuraÉ—iyya

Aƙalla tsoffin gwamnoni 58 ne ake zargin sun wawure kuma sun yi almubazzarancin jimillar naira Tiriliyan 2.187 a cikin shekaru 25 tun komawa mulkin...