Saudiya ta kashe mutane biyar da aka samu da laifin ta’addanci

Kasar Saudiya ta sanar da zartar da hukuncin kisa kan wasu mutane biyar yan kasar hudu da kuma wani dan kasar Masar bayan da aka same su da laifin kai wani mummunan hari a wurin ibada.

Kamfanin dillancin labarai na Saudiya ya bayyana cewa an kai harin ne a yankin Al-Ahsa inda mutane biyar suka mutu wasu kuma da dama suka jikkata.

Kafafen yada labarai na kasar da suka bada rahoton ba su bayyana lokacin da abun ya faru ba ko kuma wurin ibadar da aka kai harin.

Dan kasar Masar din shi ne aka samu da laifin harbin jami’an tsaro tare da yunkurin tayar da bom sai kuma aikata laifin shiga kungiyar yan ta’adda.

Ana zargin mutane uku da taimaka masa wajen shiryawa da tsara harin.

Mutum na hudu an same shi da laifin kin sanar da hukuma kan shirin kai harin da kuma laifin zuga wasu su shiga kungiyar ta’addanci.

More News

Ƴan sanda sun kama mutane 50 kan rikicin da ya faru a wata kasuwa a Lagos

Rundunar Æ´an sandan jihar Legas ta kama mutane sama da 50 da ake zargin suna da hannu rikicin da ya faru a kasuwar Ile...

Ƴan Sanda sun kama wanda ya shirya kai harin jirgin ƙasar Abuja-Kaduna a shekarar 2022

Rundunar ƴan sandan Najeriya ta ce jami'anta sun kama wani mutum mai suna Ibrahim Abdullahi wanda ake zargi da kitsa harin jirgin ƙasar da...

Sojoji Sun Ceto Mutane Daga Hannun Masu Garkuwa Da Mutane A Filato

Dakarun rundunar Operation Safe Haven dake aikin tabbatar da tsaro a jihar Filato da wani É“angare na jihar Kaduna sun samu nasarar ceto mutane...

Matatar Mai Ta Kaduna Za Ta Fara Aiki A Ƙarshen 2024

Kamfanin Kaduna Refining and Petrochemical Company KPRC ya ce matatar mansa za ta fara aiki a shekarar 2024. Mustapha Sugungun managan matatar man ta KRPC...