Sarkin Musulmi Ya Yi Kira A Fara Duba Watan Ramadan Daga Ranar Lahadi

Mai alfarma Sarkin Musulmi, Alhaji Sa’ad Muhammad Abubakar ya yi kira ga al’ummar Musulmi da su fara duban watan Ramadan ranar Lahadi.

Sarkin Musulmin ya sanar da haka ne cikin wata sanarwa da, Salisu Shehu sakataren majalisar koli ta addinin Muslunci ta ƙasa ya fitar.

Sanarwar ta ce za a fara azumin Ramadan kai tsaye ranar Talata matukar ba a ga watan ba a ranar Lahadi.

Kwamitin ganin wata na Æ™asa shi ne ya bayar da shawarar fara duban watan a ranar Lahadi wacce tayi dai-dai da 29 ga watan Sha’aban shekarar 1445 bayan hijira.

Sarkin Musulmin ya roƙi Musulmi masu hannu da shuni dake ƙasarnan da su bada sadaka ga mutanen da basu da ƙarfi da suke maƙotaka da su a lokacin azumin dama bayan azumi.

More News

Gwamnatin Adamawa Ta Ƙara Hutun Ɗaliban Makarantu Saboda Annobar Cutar Ƙyanda

Gwamnatin jihar Adamawa ta tsawaita lokacin komawar É—aliban jihar makarantunsu domin fara  zangon karatu na uku saboda annobar cutar Æ™yanda. A wata sanarwa ranar Litinin,...

Sojan Jamhuriyar Nijar sun kama Gawurtaccen ÆŠan Fashin dajin Najeriya Kachalla Mai Daji

Dakarun sojan Jamhuriyar Nijar sun samu nasara kama gawurtaccen É—an fashin dajin nan mai suna Kachalla Mai Daji a garin Illela dake kan iyakar...

Ƴan Fashin Daji Sun Kashe Mutane 7 A Jihar Kebbi

Mutane 7 aka bada rahoton ƴan fashin daji sun kashe  a garin Tudun Bici dake ƙaramar hukumar Danko Wasagu ta jihar Kebbi. A cewar mazauna...

Tsoffin gwamnoni sun wawashe sama da naira tiriliyan 2 tun komawa dimokuraÉ—iyya

Aƙalla tsoffin gwamnoni 58 ne ake zargin sun wawure kuma sun yi almubazzarancin jimillar naira Tiriliyan 2.187 a cikin shekaru 25 tun komawa mulkin...