Babban Sifetan Yan sandan Najeriya, Kayode Egbetokun ya tura karin jami’an yan sanda zuwa jihar Benue biyo bayan harin da aka kai kan wasu bankunan kasuwanci daban-daban guda hudu a jihar.
A ranar Juma’a wasu yan bindiga suka kai farmaki garin Otukpo dake jihar inda suka shafe sama da awanni biyu suna fashi a bankunan huɗu.
Andrew Aganga wani mazaunin garin ya ce yan fashin sun kuma kai hari kan ofishin yan sanda dake kusa da bankunan.
Da yake tabbatar da faruwar haka mai magana da yawun rundunar yan sandan Najeriya, Olamuyiwa Adejobi ya tabbatar da cewa John Adikwu baturen yan sanda na Otukpo da karin wasu yan sanda uku sai kuma farar hula uku na daga cikin waɗanda aka kashe a harin.
Ya ƙara da cewa an kashe biyu daga cikin ƴan bindigar.
Adejobi ya ce babban sifetan yan sandan ya bada umarnin gudanar da cikakken bincike domin gano waɗanda suka kai harin.