Rundunar yan sanda ta musalta zargin yin garkuwa da yan sanda 10

Kwamishinan yan sandan jihar Kogi, Edward Egbuka ya musalta labaran dake yawo a gari cewa yansanda 10 ake zargin yan bindiga sun yi garkuwa da su lokacin da suke dawowa daga aikin zabe a jihar Osun.

Ya ce rundunar ta gano dukkanin yan sandan inda ya tabbatar da cewa yan bindiga sun kai hari kan ayarin motocinsu a ranar Lahadi amma babu wanda suka yi garkuwa da shi.

Ya kara da cewa dukkanin yan sandan sun tsere cikin daji da aka kai musu harin saboda gudun kada ayi garkuwa da su.

Ya ce da kura ta lafa dukkanin yansandan da ake zargin an sace sun fito daga maboyar su inda suka hadu da abokan aikinsu a jihar Nasarawa.

Yan sandan na kan hanyarsu ne ta zuwa jihar Nasarawa lokacin da lamarin ya faru.

More News

Mai magana da yawun Tinubu ya ajiye aikinsa na wani lokaci

Mai ba shugaban kasa shawara na musamman kan harkokin yada labarai Ajuri Ngelale ya ajiye aikinsa na wani lokaci domin tunkarar matsalar lafiya.Mista Ngelale...

Ali Jita ya koma jam’iyar APC daga NNPP

Mataimakin shugaban majalisar dattawa dattawa, Sanata Barau Jibrin ya karɓi fitaccen mawakin Kannywood, Aliyu Isa Jita daga jam'iyar NNPP ya zuwa jam'iyar APC. Ali Jita...

An yi jana’izar mutumin da ya Æ™irÆ™iri tutar Najeriya

Iyalan marigayi, Pa Taiwo Akinkumi mutumin da ya ƙirƙiro tutar Najeriya sun yi bikin binne shi bayan da gwamnatin tarayya ta gaza cika alƙawarin...

‘Za a Æ™ara wa Æ´an bautar Æ™asa na NYSC alawus’

Babban daraktan hukumar yi wa kasa hidima ta kasa (NYSC) Birgediya Janar Yushau Ahmed, ya tabbatar wa ‘yan bautar kasar cewa za a kara...