Rundunar yan sanda ta musalta zargin yin garkuwa da yan sanda 10

Kwamishinan yan sandan jihar Kogi, Edward Egbuka ya musalta labaran dake yawo a gari cewa yansanda 10 ake zargin yan bindiga sun yi garkuwa da su lokacin da suke dawowa daga aikin zabe a jihar Osun.

Ya ce rundunar ta gano dukkanin yan sandan inda ya tabbatar da cewa yan bindiga sun kai hari kan ayarin motocinsu a ranar Lahadi amma babu wanda suka yi garkuwa da shi.

Ya kara da cewa dukkanin yan sandan sun tsere cikin daji da aka kai musu harin saboda gudun kada ayi garkuwa da su.

Ya ce da kura ta lafa dukkanin yansandan da ake zargin an sace sun fito daga maboyar su inda suka hadu da abokan aikinsu a jihar Nasarawa.

Yan sandan na kan hanyarsu ne ta zuwa jihar Nasarawa lokacin da lamarin ya faru.

More from this stream

Recomended

Kotun Tarayya Ta Tabbatar Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC

Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta tabbatar da shugabancin jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) Æ™arÆ™ashin jagorancin tsohon shugaban majalisar dattawa, David Mark. Kotun ta yi watsi da Æ™arar da É—an majalisar wakilai, Leke Abejide, ya shigar kan shugabancin jam’iyyar, inda ta bayyana cewa lamarin ya shafi harkokin cikin gida na jam’iyyar siyasa. Mai […]