Rundunar yan sanda ta musalta zargin yin garkuwa da yan sanda 10

Kwamishinan yan sandan jihar Kogi, Edward Egbuka ya musalta labaran dake yawo a gari cewa yansanda 10 ake zargin yan bindiga sun yi garkuwa da su lokacin da suke dawowa daga aikin zabe a jihar Osun.

Ya ce rundunar ta gano dukkanin yan sandan inda ya tabbatar da cewa yan bindiga sun kai hari kan ayarin motocinsu a ranar Lahadi amma babu wanda suka yi garkuwa da shi.

Ya kara da cewa dukkanin yan sandan sun tsere cikin daji da aka kai musu harin saboda gudun kada ayi garkuwa da su.

Ya ce da kura ta lafa dukkanin yansandan da ake zargin an sace sun fito daga maboyar su inda suka hadu da abokan aikinsu a jihar Nasarawa.

Yan sandan na kan hanyarsu ne ta zuwa jihar Nasarawa lokacin da lamarin ya faru.

More News

Zanga-zanga: An jibge Æ´an sanda 4200 a Abuja

Rundunar Æ´an sandan birnin tarayya Abuja ta tura Æ´an sanda 4200 gabanin zanga-zangar da za a gudanar a cikin watan Agusta. Kamar yadda masu shirya...

Kamfanin NNPC ya shirya daukar karin ma’aikata

Kamfanin mai na Nigerian National Petroleum Company Limited ya shirya daukar karin ma’aikata.Kakakin kamfanin na NNPC, Olufemi Soneye, ya tabbatar da hakan a wata...

Ya kamata matasa su yi haÆ™uri zanga-zanga ba ita ce mafita ba – Sarkin Zazzau

Sarkin Zazzau, Mai Martaba Ahmed Nuhu Bamalli ya ce matasa su ƙara haƙuri da gwamnatin tarayya su janye zanga-zangar da suka shirya gudanarwa a...

Zanga-zanga: Tinubu ya gana da gwamnonin APC

Shugaban ƙasa, Bola Ahmad Tinubu ya gana da gwamnonin da aka zaɓa ƙarƙashin jam'iyar APC. Taron ganawar da aka gudanar a fadar shugaban ƙasa ta...