Rikici kan abinci ya sa wani magidanci kashe matarsa.

Yan sanda a jihar Edo sun kama wani mutum mai suna, Salami Anedu ɗan shekara 21 kan zargin kashe matarsa sakamakon saɓani sa suka samu akan abinci.

Mutumin da ake zargi na daga cikin jerin masu laifuka da rundunar yan sandan jihar ta kama kuma ta gabatarwa da manema labarai su.

Mai magana d yawun rundunar, SP Chidi Nwabuzor ya ce ofishin yan sanda na Fugar ne suka kama mai laifin a ranar 30 ga watan Agusta.

Ya ce wani mutum mai suna, Aluaye Momoh a ranar 29 ga watan Satumba ya kai kara wurin yan sanda cewa wani mutum Salami Anedu yayi amfani da sanda ya kashe matarsa, Esther Friday mai shekaru 21 a gidansu dake kauyen Ugbekpe a jihar Edo kan sabani da suka samu akan al’amuran gida.

Mai magana da yawun rundunar ya ce wanda ake zargi ya daki matarsa da katako a lokacin saɓanin inda kuma hakan ya yi sanadiyar ajalinsa.

Sai dai Salami ya musalta aikata kisan kan inda ya ce matar tasa dama bata da lafiya kafin rikicin na su kuma ta mutu ne a gidansu.

More News

An sake gano gawar wani shugaban Fulani da ya ɓata a jihar Filato

An gano gawar wani Arɗon Fulani, Umar Ibrahim da ya ɓace a cikin wata rijiya dake kauyen Jokom a ƙaramar hukumar Mangu ta...

An kama Æ´an kungiyar IPOB 18 da ake zargi da kisan Æ´an sanda

Rundunar yan sandan jihar Imo ta kama mutane 18 da ake zargi da zama yan kungiyar IPOB da suke da hannu a kisan Æ´an...

Kotun ɗaukaka ƙara ta tabbatar da zaɓen gwamnan jihar Sokoto

Kotun ɗaukaka ƙara dake Abuja ta tabbatar da zaɓen, Ahmed Aliyu a matsayin gwamnan jihar Sokoto. Rukunin alkalan kotun su uku sun yi watsi da...

Kotun ɗaukaka ta soke zaɓen shugaban majalisar dokokin jihar Kaduna

Kotun ɗaukaka ƙara dake Abuja, ta soke zaɓen kakakin majalisar dokokin jihar Kaduna, Yusuf Liman. Alkalan kotun uku sun bayar da umarni da a sake...