Rikici kan abinci ya sa wani magidanci kashe matarsa.

Yan sanda a jihar Edo sun kama wani mutum mai suna, Salami Anedu ɗan shekara 21 kan zargin kashe matarsa sakamakon saɓani sa suka samu akan abinci.

Mutumin da ake zargi na daga cikin jerin masu laifuka da rundunar yan sandan jihar ta kama kuma ta gabatarwa da manema labarai su.

Mai magana d yawun rundunar, SP Chidi Nwabuzor ya ce ofishin yan sanda na Fugar ne suka kama mai laifin a ranar 30 ga watan Agusta.

Ya ce wani mutum mai suna, Aluaye Momoh a ranar 29 ga watan Satumba ya kai kara wurin yan sanda cewa wani mutum Salami Anedu yayi amfani da sanda ya kashe matarsa, Esther Friday mai shekaru 21 a gidansu dake kauyen Ugbekpe a jihar Edo kan sabani da suka samu akan al’amuran gida.

Mai magana da yawun rundunar ya ce wanda ake zargi ya daki matarsa da katako a lokacin saɓanin inda kuma hakan ya yi sanadiyar ajalinsa.

Sai dai Salami ya musalta aikata kisan kan inda ya ce matar tasa dama bata da lafiya kafin rikicin na su kuma ta mutu ne a gidansu.

More News

Ƴan sanda sun kama mutane 50 kan rikicin da ya faru a wata kasuwa a Lagos

Rundunar Æ´an sandan jihar Legas ta kama mutane sama da 50 da ake zargin suna da hannu rikicin da ya faru a kasuwar Ile...

Ƴan Sanda sun kama wanda ya shirya kai harin jirgin ƙasar Abuja-Kaduna a shekarar 2022

Rundunar ƴan sandan Najeriya ta ce jami'anta sun kama wani mutum mai suna Ibrahim Abdullahi wanda ake zargi da kitsa harin jirgin ƙasar da...

Sojoji Sun Ceto Mutane Daga Hannun Masu Garkuwa Da Mutane A Filato

Dakarun rundunar Operation Safe Haven dake aikin tabbatar da tsaro a jihar Filato da wani É“angare na jihar Kaduna sun samu nasarar ceto mutane...

Matatar Mai Ta Kaduna Za Ta Fara Aiki A Ƙarshen 2024

Kamfanin Kaduna Refining and Petrochemical Company KPRC ya ce matatar mansa za ta fara aiki a shekarar 2024. Mustapha Sugungun managan matatar man ta KRPC...