Ortom ya shawarci Yahaya Bello da ya miƙa kansa ga EFCC

Tsohom gwamnan jihar Binuwai, Samuel Ortom, a ranar Lahadin da ta gabata, ya bukaci takwaransa na jihar Kogi, Yahaya Bello, da ya fito daga maboyarsa, ya amsa kararsa da hukumar yaki da masu yi wa tattalin arzikin kasa zagon kasa ta EFCC.

Bello dai ya dade yana takun saka tsakaninsa da hukumar yaki da cin hanci da rashawa ta EFCC, inda ta bayyana cewa ana nemansa ne bayan da ya kasa gurfana a gaban kotu a babban kotun tarayya da ke Abuja inda hukumar yaki da cin hanci da rashawa ta shigar da kara a gaban kotu na tuhumarsa da laifin zamba na N80.2bn.

Hukumar shige da fice ta Najeriya ta kuma sanya Bello cikin jerin sunayen, inda ta bayar da umarnin a kama shi a duk inda aka same shi.

More News

Peter Obi Ya Ziyarci Mutanen Da Su Ka Ƙone Sakamakon Wutar Da Wani Ya Cinnawa   Masallaci A Kano

Ɗan takarar shugaban ƙasa  a zaɓen 2023 ƙarƙashin jam'iyar Labour Party (LP) Peter Obi ya ziyarci mutanen da wani matashi ya cinnawa wuta a...

An sanar da zaman makoki na kwana biyar saboda mutuwar shugaban kasa a Iran

Jagoran juyin juya halin Musulunci na Iran Ayatollah Ali Khamenei ya sanar da zaman makoki na kwanaki biyar saboda rasuwar shugaban kasar Ibrahim Raisi...

Najeriya za ta dena shigo da man fetur a cikin watan Yuni – Dangote

Aliko Dangote mutumin da ya fi kowa arziki a Nahiyar Afirka ya ce Najeriya za ta daina shigo da man fetur a cikin watan...

An ceto mutane 9 daga wani ginin bene da ya ruguzo a jihar Niger

Mutane 9 aka samu nasarar cetowa daga wani ginin bene mai hawa ɗaya da ya ruguzo a yankin Sabon Gwari dake garin Minna babban...