Asalin hoton, KADUNA STATE GOVERNMENT
Lauyoyi sun cacaki el-Rufai a tuwita
Zargin tauye haƙƙi kusan shi ne abin da ake tafka muhawara a kai kan gwamnan jihar Kaduna Nasir Elrufa’i tun safiyar wannan Juma’ar a shafukan sada zumunta a Najeriya.
Wannan kuwa ya biyo bayan gayyatar da ƙungiyar lauyoyi ta ƙasa ta yi wa gwamnan domin halartar taronta na ƙasa da ta shirya gudanarwa, wanda ya gamu da suka.
Sai dai abu kamar wasa wannan batu ya zama babba domin tun a jiya Alhamis ƙungiyar Lauyoyin ta sanar da janye gayyatar da ta yi wa gwamnan sakamakon adawar da wasu lauyoyi suka rinka nuna wa.
Wannan batu a yanzu ya kasance abin da ke jan hankali inda wasu ke suka wasu kuma ke yaba matakin ƙungiyar lauyoyin.
The National Executive Committee of the Nigerian Bar Association at its ongoing meeting resolves that the invitation to the Kaduna State Governor, H.E. Nasir El-Rufai by the 2020 Annual General Conference Planning committee be withdrawn and decision communicated to the Governor.
— Nigerian Bar Association (@NigBarAssoc) August 20, 2020
Karshen labarin da aka sa a Twitter, 1
Kungiyar lauyoyin ta jadada cewa ta yanke wannan hukunci ne biyo bayan zanga-zangar da wasu lauyoyi suka yi kan gayyatar.
Da fari dai wani lauya mai suna Usani Odum ne ya soma ƙaddamar da takardar koke ta intanet inda ya nemi ƙungiyar ta janye gayyatar da ta yi wa gwamnan.
Sannan daga bisani wasu lauyoyi suka rinƙa aike sako cewa za su bijire wa taron in dai El-Rufai na cikin waɗanda aka gayyata domin gabatar da jawabi.
Dear @NigBarAssoc, I just ran through the list of speakers in the forthcoming virtual conference and Gov. El-Rufai’s name is on the list. I’ll be withdrawing my attendance and cancelling my registration for the conference.
Thank you.
— Itong Washington (@itongwashington) August 17, 2020
Karshen labarin da aka sa a Twitter, 2
Shi ma Femi Falana babban lauya mai fafutukar kare hakkin dan adam na cikin lauyoyin da wasikar da ya rubuta ta nuna adawa da halarta El-rufa’i a taron ke ta yawo a shafin intanet.
Wasu daga cikin bayanan da ke kunshe a wasiƙar sun hada da zargin cewa gwamnan yana ”bijirewa umarni da raina kotu”. ”Kuma gayyatar irin wadanan mutane ya saɓa dokokin kungiyar lauyoyi.”
Sannan wasiƙar ta kara da cewa ”ƙungiyar ba za ta ragawa masu riƙe da ofisoshin gwamnati da ke da ra’ayin rashin hukunta masu laifi a ƙasa ba”.
Asalin hoton, Twitter
Asalin hoton, Twitter
Masu ƙoken akasari na zargin gwamnan da gazawa wurin shawo kan rikicin Kudancin Kaduna da kuma take haƙƙn bil adama.
Kuma ragargazar gwamnan da aka rinƙa yi ta tilasta wa kungiyar lauyoyi yanke shawarar janye goron gayyatar da aka tura wa gwamnan.
Sai dai yayin da wasu ke nuna adawa da halartar El-rufai wannan taro wasu lauyoyin kuma cewa suke suna bayan gwamnan.
I know it may not make any difference but I’m boycotting the virtual NBA AGC for the withdrawal of @elrufai as a guest speaker based on frivolous and unsubstantiated allegations #IStandWithElrufai
— halima gachi (@halimagachi) August 21, 2020
Karshen labarin da aka sa a Twitter, 3
Halima Gaci ta ce: Na san ba zai sauya wannan abu ba amma dai na janye daga halartar taron lauyoyi ta ƙasa da za a gudanar a intanet saboda janyewar @elrufai a matsayin bakon da zai yi jawabi na musamman kan dalilai da zarge-zarge marasa inganci da hujja #IStandWithElrufai
Amma a nasu bangaren masu sharhi kamar Dr. Hakeem Baba Ahmed ya ce janye gayyatar da aka yi wa gwamnan El-Rufai ta hana shi magana a wajen wannan taro ya saɓa ƙa’idar ƙungiyar da ya kamata a ce ta ƙarfafa ba da dama a saurari mutum da kuma damar yi masa tambayoyi.
Decision of NBA to withdraw invitation to Gov el-Rufai to speak at its Convention is a disservice to an org that should champion fair hearing,free speech and tolerance. It deprives lawyers opportunity to interrogate a colleague in the eye of a storm,and has set a bad precedent.
— Dr. Hakeem Baba-Ahmed. (@baba_hakeem) August 20, 2020
Karshen labarin da aka sa a Twitter, 4
Wani Bashir Dabo kuma yana cewa: ”NBA ta jefa kanta cikin yanayi mara bullewa kan shawarar da ta yanke kan Mal el-Rufa’i. Kungiyar ta ba da kanta kan martabar da take da ita saboda dalilai na siyasa. Ƙungiyar ta shigar da kanta cikin kazamar siyasa irin ta Najeriya.”
NBA has set a dangerous precedent and trap for itself with this ill-thought-out decision on Malam el-Rufai. The body has forfeited its noble etiquette of reason for political correctness.
It has been dragged into the murky waters of Nigeria’s clannish politics.— Bashir Dabo (@Bashir_Dabo) August 20, 2020
Karshen labarin da aka sa a Twitter, 5
Mutane da dama ne suka sanya hannu a ƙorafin buƙatar ƙungiyar lauyoyi na cire sunan gwmanan El-Rufa’i cikin baƙin da za su yi jawabi a taronta na ƙasa da ke soma wa a ranar 24 ga watan Agustan 2020.
Lauyoyin na cewa ƙarƙashin mulkin el-Rufa’i, an cafke mutane da dama ta haramtacciyar hanya, wasu daga cikinsu akwai fitattun masu suka, Abubakar Idris, wanda aka fi sani da Dadiyata, wanda ya ɓace babu labarinsa.
Tuni da ƙungiyoyin irin su SERAP mai fafutukar kare cin hanci ta ce ta yi marhaba da matakin janye gayyatar da aka yi wa El-Rufai, sannan ta shawarci ƙungiyar kar ta gayyaci ko da mutum guda daga gwamnatin da ‘yan majalisa har sai Shugaba Buhari ya mutunta umarnin kotuna.
BREAKING: We welcome decision by @NigBarAssoc to withdraw its invitation to Kaduna State Governor Nasir el-Rufai on ground of poor human rights record.
We also call on NBA NOT to invite @NigeriaGov /its reps to its events until President Buhari obeys ALL outstanding court orders
— SERAP (@SERAPNigeria) August 20, 2020
Karshen labarin da aka sa a Twitter, 6
Ita ma ƙungiyar ƴan shi’a ta IMN ta yaba wa mataƙin lauyoyin na janye gayyatar da ta yi wa gwamnan a cikin wata sanarwa da kakakinta Ibrahim Musa ya aike wa BBC ranar Juma’a. Sanarwar ta ce gwamnan bai cancanci halartar taron ba.
Sai dai ƙungiyar lauyoyi reshan jihar Jigawa ta yi barazanar cewa babu daya daga cikin mambobinta da za su halarci taron muddin el-Rufa’i ba zai je taron ba.
Kazalika ƙungiyar kare haƙƙin Musulmi wato Muric ta yi kira ga lauyoyin arewacin Najeriya su kaurace wa taron saboda rashin dacewar da ta ce an yi wa gwamnan.
Wasu labaran da zaku so karantawa
Martanin El-Rufai
Asalin hoton, Elrufai
Gwamnatin Kaduna ta wallafa a Tuwita amincewar gwamna El Rufa’i da goron gayyatar da NBA ta yi wa gwamnan na Kaduna bayan ƙungiyar lauyoyin ta janye gayyatar.
Sannan gwamnatin ta mayar da martani ga matakin janye gayyatar inda ta ce bai kamata babbar ƙungiya kamar NBA ta amince da wani zance ba daga wani ɓangare kan batun da ya shafi ƙasa ba.
Gwamnatin ta ce kalaman ɓata suna da wasu mambobin ƙungiyar suka yi wani abu ne na daban kuma za ta mayar da martani.
Zuwa yanzu gwamnatin Kaduna ko Gwamna El Rufa’i ba su mayar da martani ba ga ƙungiyar ƴan shi’a.
Sharhi
Wannan yanayi da ake ciki na nuna alamomin rarrabauwar kawuna tsakanin lauyoyi da wasu masu sharhi.
Yayin da ake gani kamar kusan taron dangi aka yi wa el-Rufai a shafukan sada zumunta, wasu nuna goyon baya suka yi da nanata cewa suna ɓangaren gwamnan.
Yanzu abin jira a gani shi ne yadda wannan ce-ce-ku-cen zai wanye tsakanin lauyoyin, ko da yake akwai masu cewa siyasa ta shiga zance.
Sannan akwai masu cewa idan har za a hana el-Rufai zuwa taron to kamata ya yi wannan hukunci ya hau kan gwamnan Nyesom Wike na Ribas domin halayensu na da kamanceceniya.