Najeriya ta gargadi ƴan ƙasarta game da zuwa Nijar

Kwanturolan hukumar shige da fice ta Najeriya (NIS) mai kula da rundunar Jibia ta musamman a jihar Katsina, Mustapha Sani, ya gargadi ‘yan Najeriya kan yin balaguro zuwa Jamhuriyar Nijar.

Hakan dai ya zo ne sakamakon rikicin jamhuriyar Nijar bayan juyin mulkin da aka yi a kasar.

Kasar ta Afirka ta Yamma ta fuskanci takunkumi sakamakon kasancewerta karkashin mulkin soja.

Ya yi wannan jawabi ne a ranar Alhamis a wani bikin hadin gwiwa da hukumar NIS ta jihar Katsina domin bikin cika shekaru sittin.

More News

Ƴansanda sun kama muggan ƴan fashi da makami

Jami’an hukumar ‘yan sanda reshen Elemoro reshen jihar Legas sun kama wasu mutane uku da ake zargi da hannu a fashi da makami a...

An kama wasu mutane biyu da hodar ibilis a Lagos

Rundunar ƴan sandan jihar Lagos ta sanar da kama wasu mutane biyu da aka samu ɗauke da ƙunshin hodar ibilis mai yawan gaske. Mai magana...

Ƴan sanda sun kama wani mutum ɗauke da bindigogi 20 a Kaduna

Rundunar ƴan sandan jihar Kaduna ta ce jami'anta sun kama wani  riƙaƙƙen mai safarar bindiga inda aka same shi da bindigogin AK-47 ƙirar gida...

Kwankwaso ya bada tallafin miliyan ₦50 ga mutanen da ambaliyar Borno ta shafa

Tsohon gwamnan jihar Kano kuma jagoran jam'iyar NNPP, Sanata Rabi'u Musa Kwankwaso ya bada tallafin naira miliyan 50 ga mutanen da ambaliyar ruwa a...