Zikirillah Hassan, shugaban hukumar Aikin Hajji Ta Kasa, NAHCON ya ce kamfanonin jiragen sama da aka amince su ɗauki alhazan bana zuwa kasar Saudiyya sun amince ayi karin dala $250 kan kuɗin kowace kujera.
Shugaban ya bayyana haka ne a Abuja ya yi wani taron horarwa da aka shiryawa ma’aikatan NAHCON, na hukumomin alhazan jihohi da kuma na masu zaman kansu da aka fi sani da yan jirgin yawo.
Hassan ya tabbatar da cewa kuɗin karin ba zai fito daga hannun alhazan ba.
Ya ce kamfanonin jiragen saman Air Peace, Max Air,Azman da kuma Aero Contractors su ne suka gabatar da wannan bukatar saboda rikicin da ake fama da shi a kasar Sudan wanda ya jawo karin lokaci mai tsawo kafin a isa Saudiyya.
Tun kafin wannan karin mutane da dama sun koka kan yadda kuɗin kujerar aikin hajjin bana ya ƙaru sosai.