Buhari ya bayyana hakan ne a wata sanarwa da kakakinsa Garba Shehu ya fitar a ranar Juma’a sa’o’i bayan rasuwarsa.
Janar Attahiru ya rasu ne a wani hadarin jirgi da ya auku a kusa da filin tashin jirage da ke Kaduna a arewa maso yammacin kasar.
“Hadarin jirgin, ya yi mana kwaf daya a makasa, a kuma daidai lokacin da dakarunmu suka samo bakin zaren kawo karshen matsalar rashin tsaro da kasar ke fuskanta.” Buhari ya ce a sanarwa ta Shehu wacce ya wallafa a shafin Twitter.
Buhari wanda ya yi addu’a ga mamatan, ya sha alwashin ba za a manta da irin saudakarwar da suka yi ba.
A watan Janairu, Buhari ya nada Janar Attahiru, wanda ya gaji Janar Tukur Buratai tare da sauran hafsoshin sojojin kasar.
Wannan shi ne karo na uku a wannan shekara da jirgin sojin Najeriya ke yin hatsari ko ya bata a neme shi a rasa.
A halin da ake ciki fadar shugaban kasar, ta fitar da sunayen mutum 11 da suka mutu a hatsarin jirgin:
– Lt Gen. I. Attahiru
– Brig Gen. MI Abdulkadir
– Brig Gen. Olayinka
– Maj. LA Hayat
– Maj. Hamza
– SGT Umar
Matuka Jirgin Da Masu Hidima
– FLT LT TO Asaniyi
– FLT LT AA Olufade
– ACM Oyedepo