Mutum 9,007 Suka Warke Daga COVID-19 a Najeriya

Sabbin alkaluman da hukumar dakile yaduwar cututtuka ta NCDC a Najeriya ta fitar sun nuna cewa karin daruruwan mutane sun kamu da cutar COVID-19 a kasar.

A cewar hukumar, mutum 490 ne cutar ta harba wanda hakan ya mayar da gaba dayan adadin zuwa 24,567.

Daga jihohi 20 na kasar aka samu sabbin alkaluman, kuma har yanzu jihar Lagos ce ke kan gaba a yawan wadanda suka kamu da cutar wadda coronavirus ke janyowa, inda yanzu ta sake samun mutum 118. Sai jihar Delta da ke bin ta da mutum 84.

Sauran jihohin da aka samu karin wadanda suka kamu da cutar sun hada da Ebonyi inda aka samu mutum 68, 56 a birnin tarayya Abuja, 39 a Plateau, 29 a Edo, 21 a Katsina, 13 a Imo, 12 a Ondo, 11 a Adamawa, 8 a Osun, 8 a Ogun, 6 a Rivers, 5 a Kano, 3 a Enugu, 3 a Bauchi, 3 a Akwa Ibom, 1 a Kogi, 1 a Oyo, 1 a Bayelsa.

A sanarwar da hukumar ta wallafa a shafinta na Twitter a daren ranar Lahadi 28 ga watan Yuni, ta kuma bayyana cewa mutum 9,007 suka warke daga cutar yayin da mutum 565 suka mutu.

More News

Najeriya za ta dena shigo da man fetur a cikin watan Yuni – Dangote

Aliko Dangote mutumin da ya fi kowa arziki a Nahiyar Afirka ya ce Najeriya za ta daina shigo da man fetur a cikin watan...

An ceto mutane 9 daga wani ginin bene da ya ruguzo a jihar Niger

Mutane 9 aka samu nasarar cetowa daga wani ginin bene mai hawa É—aya da ya ruguzo a yankin Sabon Gwari dake garin Minna babban...

An yi faÉ—a tsakanin masu sayar da waya da sojoji a kasuwar Abuja

Rundunar ‘yan sandan babban birnin tarayya, ta tura jami’an leken asiri zuwa kasuwar Banex – wata kasuwar kayan lantarki da na’urorin sadarwa da ke...

Yawan Mutanen Da Suka Mutu A Wutar Da Wani Matashi Ya Cinnawa Wani Masallaci A Kano Sun  Karu Zuwa 16

Rundunar ƴan sandan jihar Kano ta ce yawan mutanen da suka mutu sakamakon wutar da wani ya cinnawa wani masallaci a ƙauyen Gadan a...