Mutum 78,000 ne suke mutuwa saboda cutar jeji duk shekara a Najeriya—ƙungiyar likitoci

Kungiyar Likitocin Radiation da Clinical Oncologists ta Najeriya (ARCON) ta ce aƙalla mutane 78,000 ne ke mutuwa sakamakon kamuwa da cutar daji a duk shekara a fadin tarayya.

Yayin da ta kuma nuna rashin jin dadin yadda ‘yan Najeriya ke da lafiyarsu, hukumar ta gabatar da cewa alkaluman da aka gudanar a halin yanzu sun nuna cewa kimanin mutane 125,000 ne ake samun rahoton bullar cutar a duk shekara a kansu a kasar.

Shugaban kungiyar, Dokta Amaka Lasebikan, wanda ya yi jawabi ga manema labarai jiya a Enugu, gabanin taronsu na kimiyya da za a fara daga yau, ya bayyana cewa, matsalar ciwon daji a Najeriya na karuwa, don haka akwai bukatar gwamnati, daidaikun mutane da masu bayar da lafiya su tashi tsaye don magance matsalar.

Ƙungiyar ta ɗaura laifin rashin daidaiton samun kulawar cutar kansa, wanda a cewarta, ya fallasa majinyata da dama ta fuskar bambance-bambancen zamantakewa da tattalin arziki.

More News

Gwamnatin Abia za ta fara biyan albashi mafi maranci na naira 70,000 a watan Oktoba

Gwamnatin Jihar Abia ta sanar da cewa za ta fara biyan sabon albashi mafi karanci na naira 70,000 ga ma’aikatanta daga watan Oktoba 2024.Kwamishinan...

Sojoji sun lalata haramtattun matatun mai 32 a yankin Neja Delta

Dakarun sojan Najeriya na runduna ta 6 dake Fatakwal sun samu nasarar lalata haramtattun matatun man fetur 32 tare da ƙwace lita 250,000 na...

An gudanar da bikin cikar Kwankwaso shekara 68.

Tarin magoya baya da kuma abokanan siyasar tsohon gwamnan jihar Kano, Sanata Rabi'u Kwankwaso ne suka halarci taron lakca da aka shirya domin bikin...

Faruk Lawan ya kammala zaman gidan yarin Kuje

An sako tsohon ɗan majalisar wakilai ta tarayya, Hon Faruk Lawan daga gidan yarin Kuje bayan da ya kammala zaman gidan yarin na shekaru...