Mutane biyu sun mutu wasu da dama sun jikkata a ruftawar gini a Abuja

Mutane da dama ne aka samu nasarar cetowa daga cikin baraguzan wani ginin bene da ya ruguzo a birnin tarayya Abuja.

Lamarin ya faru ne Layin Lagos dake kauyen Garki a Garki dake Abuja da tsakar daren ranar Laraba.

A cewar wata majiya dake wurin da lamarin ya faru akalla mutane 37 aka samu nasarar cetowa daga cikin baraguzan ginin inda aka kai su asibiti domin samun kulawa.

Kawo yanzu dai mutane biyu aka tabbatar da sun mutu a lamarin.

Hukumomin birnin dai basu fitar da wata sanarwa ba kan faruwar lamarin amma hakan na zuwa ne kasa da mako guda bayan da Nyesom Wike ya kama aiki a matsayin sabon ministan Abuja inda ya ci alwashin kawo sauye sauye da dama a birnin.

More News

Gwamnatin Abia za ta fara biyan albashi mafi maranci na naira 70,000 a watan Oktoba

Gwamnatin Jihar Abia ta sanar da cewa za ta fara biyan sabon albashi mafi karanci na naira 70,000 ga ma’aikatanta daga watan Oktoba 2024.Kwamishinan...

Sojoji sun lalata haramtattun matatun mai 32 a yankin Neja Delta

Dakarun sojan Najeriya na runduna ta 6 dake Fatakwal sun samu nasarar lalata haramtattun matatun man fetur 32 tare da ƙwace lita 250,000 na...

An gudanar da bikin cikar Kwankwaso shekara 68.

Tarin magoya baya da kuma abokanan siyasar tsohon gwamnan jihar Kano, Sanata Rabi'u Kwankwaso ne suka halarci taron lakca da aka shirya domin bikin...

Faruk Lawan ya kammala zaman gidan yarin Kuje

An sako tsohon É—an majalisar wakilai ta tarayya, Hon Faruk Lawan daga gidan yarin Kuje bayan da ya kammala zaman gidan yarin na shekaru...