Mayaƙan Boko Haram Biyu Sun Miƙa Kansu Ga Sojoji

Rundunar dakarun soja ta ƙasa da ƙasa wato Multi National Task Force(MNJTF) a turance shiya ta 3 dake Monguno a Najeriya ta bayar da rahoton yadda mayaƙan kungiyar Boko Haram ke cigaba da ajiye makamai suna miƙa wuya ga jami’an tsaro.

A cewar rundunar a ranar 13 ga da watan Afrilu wasu mayaƙa biyu Ahmed Isiaka da Adam Muhammad dake da shekaru 18 da 17 kowannensu suƙa miƙa wuya ga sojojin.

Matasan biyu sun fito ne daga garin Kollorom a ƙaramar hukumar Kukawa ta jihar Borno.

Sun kuma miƙawa jami’an soja harsashi na musamman guda  250 mai girman 7.62mm da kuma harsashi 50 mai girma 7.62 ƙirar NATO da kuma wasu abubuwa da dama.

Idan za a iya tunawa koda a ranar 24 ga watan Maris rundunar ta MNJTF ta bayar da sanarwar cewa wasu mayaƙan Boko Haram biyu sun miƙa wuya ga rundunar.

More News

NFF ta naɗa Finidi George a matsayin sabon kocin Super Eagle

An naɗa Finidi George a matsayin sabon mai horar da kungiyar ƙwallon ƙafar Najeriya wato Super Eagle. Hukumar ƙwallon Ƙafa ta Najeriya, NFF ita ta...

Gwamnan Edo Zai Fara Biyan 70,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

Gwamnan jihar Edo, Godwin Obaseki ya sanar da mafi ƙarancin albashi ga ma'aikatan ga ma'aikatan jihar inda za a riƙa biyan naira dubu 70,000. Gwamnan...

JAMB ta fitar da sakamakon jarabawar 2024

Hukumar shirya jarabawar shiga makarantun gaba da sakandire ta JAMB, ta fitar da sakamakon jarrabawar shekarar 2024, watau sakamakon UTME.Sama da mutane miliyan 1.94...

Ortom ya shawarci Yahaya Bello da ya miƙa kansa ga EFCC

Tsohom gwamnan jihar Binuwai, Samuel Ortom, a ranar Lahadin da ta gabata, ya bukaci takwaransa na jihar Kogi, Yahaya Bello, da ya fito daga...