Masu juyin mulkin Nijar sun ayyana sabon firaminista

Kusan makwanni biyu bayan da sojoji suka karbe mulki a Nijar, masu juyin mulkin sun nada tsohon ministan tattalin arzikin kasar Ali Mahaman Lamine Zeine a matsayin sabon Firaministan kasar.

Mai magana da yawun gwamnatin mulkin sojan ne ya bayyana hakan a gidan talabijin da yammacin jiya Litinin.

Lamine Zeine ya taba rike mukamin ministan tattalin arziki da kudi na shekaru da dama a majalisar ministocin shugaban kasar Mamadou Tandja da aka hambarar a shekara ta 2010, kuma a baya-bayan nan ya yi aiki a matsayin masani kan tattalin arziki a bankin raya Afirka a kasar Chadi, a cewar wani rahoto da kafar yada labaran Nijar ta fitar. .

A karshen watan Yuli ne sojoji suka hambarar da zababben shugaban kasar Mohamed Bazoum tare da dakatar da kundin tsarin mulki a kasar mai mutane miliyan 26.

More News

Ƴansanda sun kama muggan ƴan fashi da makami

Jami’an hukumar ‘yan sanda reshen Elemoro reshen jihar Legas sun kama wasu mutane uku da ake zargi da hannu a fashi da makami a...

An kama wasu mutane biyu da hodar ibilis a Lagos

Rundunar ƴan sandan jihar Lagos ta sanar da kama wasu mutane biyu da aka samu ɗauke da ƙunshin hodar ibilis mai yawan gaske. Mai magana...

Ƴan sanda sun kama wani mutum ɗauke da bindigogi 20 a Kaduna

Rundunar Æ´an sandan jihar Kaduna ta ce jami'anta sun kama wani  riÆ™aƙƙen mai safarar bindiga inda aka same shi da bindigogin AK-47 Æ™irar gida...

Kwankwaso ya bada tallafin miliyan ₦50 ga mutanen da ambaliyar Borno ta shafa

Tsohon gwamnan jihar Kano kuma jagoran jam'iyar NNPP, Sanata Rabi'u Musa Kwankwaso ya bada tallafin naira miliyan 50 ga mutanen da ambaliyar ruwa a...