Masu juyin mulkin Nijar sun ayyana sabon firaminista

Kusan makwanni biyu bayan da sojoji suka karbe mulki a Nijar, masu juyin mulkin sun nada tsohon ministan tattalin arzikin kasar Ali Mahaman Lamine Zeine a matsayin sabon Firaministan kasar.

Mai magana da yawun gwamnatin mulkin sojan ne ya bayyana hakan a gidan talabijin da yammacin jiya Litinin.

Lamine Zeine ya taba rike mukamin ministan tattalin arziki da kudi na shekaru da dama a majalisar ministocin shugaban kasar Mamadou Tandja da aka hambarar a shekara ta 2010, kuma a baya-bayan nan ya yi aiki a matsayin masani kan tattalin arziki a bankin raya Afirka a kasar Chadi, a cewar wani rahoto da kafar yada labaran Nijar ta fitar. .

A karshen watan Yuli ne sojoji suka hambarar da zababben shugaban kasar Mohamed Bazoum tare da dakatar da kundin tsarin mulki a kasar mai mutane miliyan 26.

More from this stream

Recomended

Trump Ya Yaba Wa Tinubu Kan YaÆ™i Da Ta’addanci A Najeriya

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya yaba wa Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, kan abin da ya bayyana a matsayin Æ™wazon jagorancinsa wajen yaÆ™i da ta’addanci da magance matsalar tsaro a Æ™asar. A cewar Fadar Shugaban Ƙasa, Trump ya bayyana hakan ne cikin wata wasiÆ™a da ya aike wa Tinubu. Ya ce yana yaba wa shugaban […]