Phil Foden ba zai fara buga wa Manchester City wasannin Premier League na bana ba, sakamakon raunin da ya yi a Euro 2020.
Foden, mai shekara 21, ba zai buga wa City kusan wasa uku ba, sune da suka hada da na Tottenham da Norwich City da kuma Arsenal.
Haka kuma da kyar ne idan dan wasan zai buga wa tawagar Ingila wasan neman gurbin shiga gasar kofin duniya a 2022 da za ta kara da Hungary cikin watan Satumba.
Ana sa ran Foden zai koma atisaye nan da kusan mako hudu da watakila ya fara buga Premier ranar Asabar 11 ga watan Satumba a fafatawa da City za ta yi da Leicester City.
Kocin kungiyar Etihad, Pep Guardiola ya tabbatar da cewar Kevin de Bruyne na jinya, wanda ya yi rauni a tawagar Belgium a karawa da Italiya a Euro 2020.
A kakar da ta kare City ta lashe Premier League, sannan ta kai karawar karshe a Champions League – Foden ya ce za su fuskanci kalubale mai zafi a kakar bana.