Majalisar Dattawan za ta fara duba sunayen wadanda Tinubu zai naɗa ministoci

Shugaban majalisar dattawa, Godswill Akpabio, zai bayyana sunayen wadanda aka nada a matsayin ministoci a zauren majalisar na wannan mako.

A ranakun Talata da Laraba da Alhamis ne ake gudanar da zaman taron majalisar dokokin kasar biyu.

An dai tada husuma a kan jinkirin da shugaba Bola Tinubu ya yi wajen kafa majalisar ministocin sa watanni biyu bayan rantsar da shi.

A wani sabon gyara ga kundin tsarin mulkin kasar na shekarar 1999, dole ne shugaban kasa da gwamnoni su mika sunayen wadanda aka zaba a matsayin ministoci ko kwamishinoni cikin kwanaki 60 da rantsar da su domin tabbatarwar majalisar dattawa.

More News

Tsoffin gwamnoni sun wawashe sama da naira tiriliyan 2 tun komawa dimokuraɗiyya

Aƙalla tsoffin gwamnoni 58 ne ake zargin sun wawure kuma sun yi almubazzarancin jimillar naira Tiriliyan 2.187 a cikin shekaru 25 tun komawa mulkin...

Ƴan sanda sun kama mutane 50 kan rikicin da ya faru a wata kasuwa a Lagos

Rundunar ƴan sandan jihar Legas ta kama mutane sama da 50 da ake zargin suna da hannu rikicin da ya faru a kasuwar Ile...

Ƴan Sanda sun kama wanda ya shirya kai harin jirgin ƙasar Abuja-Kaduna a shekarar 2022

Rundunar ƴan sandan Najeriya ta ce jami'anta sun kama wani mutum mai suna Ibrahim Abdullahi wanda ake zargi da kitsa harin jirgin ƙasar da...

Ƴansanda sun kama wanda ya kitsa harin da aka kai wa jirgin ƙasa a Kaduna

Rundunar ‘yan sandan Najeriya a ranar Alhamis, ta sanar da kame wanda ake zargin ya shirya harin da aka kai a jirgin ƙasan Abuja-Kaduna...