Fatima Mamman Daura, ‘yar makusancin Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ta ce mahaifinta bai kanainaye gwamnatin Buhari ba kamar yadda wasu ke tunani.
A hirarta da BBC, Fatima ta ce mahaifinta Mamman Daura da Shugaba Buhari sun tashi tare kuma abokansu daya don haka ne ya sa kusancinsu ya yi yawa.
Ta ce “kowa na da amini, wanda yake jin maganarsa. To aminan juna ne sosai, shi ya sa mutane ke ganin kamar ya kankane gwamnatin.”
Mamman Daura dan uwa ne na kusa ga shugaban Najeriyar – Buhari kawunsa ne – kuma duk da cewa ba shi da mukami a gwamnatin amma ana hasashen cewa yana da fada-a-ji a fadar ta shugaban kasa.
Fatima ta ce ba gaskiya ne ba zancen da ake cewa mahaifinta ya kanainaye Shugaba Buharin sai yadda ya ce ake yi, “Baba mutum ne mai kawaici, ba ya son shiga ma harkar mutane kuma bai cika yawan magana ba, kuna ma iya yin bincike akai ku gani,” a cewar Fatima.
“Na san shugaban kasa kan nemi shawararsa ammaidan ya ba da shwarar ya kan janye ne ba ya katsalandan, yana gidan yana tasbihinsa, ko mun masa maganar cewa yake mu daina damuwa ana kankare masa zunubi ne.
Ta ci gaba da cewa “ba ma jin dadin abin da ake fada a kansa amma dai mun san kasancewar sy tare ne ya sa ake masa haka albarkanci zumunci.”