Lafiya: Gwamnan Sokoto ya ba da umurnin biyan albashin watan Yuni cikin gaggawa

Gwamna Ahmed Aliyu na jihar Sokoto ya ba da umarnin a gaggauta biyan albashi da fansho na watan Yuni ga ma’aikatan jihar da ‘yan fansho.

Wannan labari ya zo ne ta bakin Sakataren Yada Labarai na Gwamnan, Abubakar Bawa.

A cewarsa an yi hakan ne da nufin gudanar da bikin Sallah ba tare da damuwa ba.

More from this stream

Recomended