Labarin Wani Dan Najeriya Mai Magana da Harsuna Takwas

Wani dan Najeriya mai suna Adedeji Odulesi ya kware a harsunan Ingilishi da Pidgin da Yoruba da Igbo da Hausa da Faransanci da Jamusanci da Sifaniyanci da kuma harshensa na asali wato Ijebu.

An haife shi ne a gidan mai da ’yan’uwa biyar, ciki har da mahaifiyarsa da mahaifinsa, wadanda dukansu ’yan kabilar ljebu ne.

A yankin Warri na jihar Delta, inda aka haife shi a shekarar 1972, Adedeji ya koyi harsunan Yarbanci, Turanci, da Pidgin.

Ya koyi harshen Hausa ne bayan da iyayensa suka koma Sakkwato a shekarar 1981. Iyalinsa sun koma Imo a karshen shekarun 1990, inda ya koyi yaren Igbo.

Ya kuma bayyana cewa ya auri Bafaranshiyar Bayerabiya kuma ya koyar da kansa Jamusanci, Sifaniyanci da Faransanci a Najeriya.

Adedeji ya shawarci iyaye da su yi magana da ’ya’yansu cikin yarensu.

More News

Tsoffin gwamnoni sun wawashe sama da naira tiriliyan 2 tun komawa dimokuraÉ—iyya

Aƙalla tsoffin gwamnoni 58 ne ake zargin sun wawure kuma sun yi almubazzarancin jimillar naira Tiriliyan 2.187 a cikin shekaru 25 tun komawa mulkin...

Ƴan sanda sun kama mutane 50 kan rikicin da ya faru a wata kasuwa a Lagos

Rundunar Æ´an sandan jihar Legas ta kama mutane sama da 50 da ake zargin suna da hannu rikicin da ya faru a kasuwar Ile...

Ƴan Sanda sun kama wanda ya shirya kai harin jirgin ƙasar Abuja-Kaduna a shekarar 2022

Rundunar ƴan sandan Najeriya ta ce jami'anta sun kama wani mutum mai suna Ibrahim Abdullahi wanda ake zargi da kitsa harin jirgin ƙasar da...

Ƴansanda sun kama wanda ya kitsa harin da aka kai wa jirgin ƙasa a Kaduna

Rundunar ‘yan sandan Najeriya a ranar Alhamis, ta sanar da kame wanda ake zargin ya shirya harin da aka kai a jirgin ƙasan Abuja-Kaduna...