Labarin Wani Dan Najeriya Mai Magana da Harsuna Takwas

Wani dan Najeriya mai suna Adedeji Odulesi ya kware a harsunan Ingilishi da Pidgin da Yoruba da Igbo da Hausa da Faransanci da Jamusanci da Sifaniyanci da kuma harshensa na asali wato Ijebu.

An haife shi ne a gidan mai da ’yan’uwa biyar, ciki har da mahaifiyarsa da mahaifinsa, wadanda dukansu ’yan kabilar ljebu ne.

A yankin Warri na jihar Delta, inda aka haife shi a shekarar 1972, Adedeji ya koyi harsunan Yarbanci, Turanci, da Pidgin.

Ya koyi harshen Hausa ne bayan da iyayensa suka koma Sakkwato a shekarar 1981. Iyalinsa sun koma Imo a karshen shekarun 1990, inda ya koyi yaren Igbo.

Ya kuma bayyana cewa ya auri Bafaranshiyar Bayerabiya kuma ya koyar da kansa Jamusanci, Sifaniyanci da Faransanci a Najeriya.

Adedeji ya shawarci iyaye da su yi magana da ’ya’yansu cikin yarensu.

More from this stream

Recomended

Kotun Tarayya Ta Tabbatar Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC

Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta tabbatar da shugabancin jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) ƙarƙashin jagorancin tsohon shugaban majalisar dattawa, David Mark. Kotun ta yi watsi da ƙarar da ɗan majalisar wakilai, Leke Abejide, ya shigar kan shugabancin jam’iyyar, inda ta bayyana cewa lamarin ya shafi harkokin cikin gida na jam’iyyar siyasa. Mai […]