Labarin Wani Dan Najeriya Mai Magana da Harsuna Takwas

Wani dan Najeriya mai suna Adedeji Odulesi ya kware a harsunan Ingilishi da Pidgin da Yoruba da Igbo da Hausa da Faransanci da Jamusanci da Sifaniyanci da kuma harshensa na asali wato Ijebu.

An haife shi ne a gidan mai da ’yan’uwa biyar, ciki har da mahaifiyarsa da mahaifinsa, wadanda dukansu ’yan kabilar ljebu ne.

A yankin Warri na jihar Delta, inda aka haife shi a shekarar 1972, Adedeji ya koyi harsunan Yarbanci, Turanci, da Pidgin.

Ya koyi harshen Hausa ne bayan da iyayensa suka koma Sakkwato a shekarar 1981. Iyalinsa sun koma Imo a karshen shekarun 1990, inda ya koyi yaren Igbo.

Ya kuma bayyana cewa ya auri Bafaranshiyar Bayerabiya kuma ya koyar da kansa Jamusanci, Sifaniyanci da Faransanci a Najeriya.

Adedeji ya shawarci iyaye da su yi magana da ’ya’yansu cikin yarensu.

More from this stream

Recomended

Trump Ya Yaba Wa Tinubu Kan Yaƙi Da Ta’addanci A Najeriya

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya yaba wa Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, kan abin da ya bayyana a matsayin ƙwazon jagorancinsa wajen yaƙi da ta’addanci da magance matsalar tsaro a ƙasar. A cewar Fadar Shugaban Ƙasa, Trump ya bayyana hakan ne cikin wata wasiƙa da ya aike wa Tinubu. Ya ce yana yaba wa shugaban […]