Kylian Mbappe: Real Madrid ta miƙa tayin yuro miliyan 160 don sayen ɗan wasan PSG

Kylian Mbappe

Asalin hoton, Getty Images

Bayanan hoto,
Yarjejeniyar Mbappe za ta zo ƙarshe a PSG nan da Yunin 2022

Real Madrid ta miƙa tayin yuro miliyan 160 don sayen ɗan wasan gaba Kylian Mbappe daga Paris St-Germain.

Ɗan wasan mai shekara 22 da ya lashe Kofin Duniya, ya koma PSG a 2017 kan kuɗi da suka kai fan miliyan 165 wanda kuma yarjejeniyarsa za ta zo ƙarshe a Yunin 2022.

Mbappe ya ci wa PSG ƙwallo 133 cikin wasa 174 da ya buga mata, inda ya lashe kofin gasar Ligue 1 uku da French Cup uku.

Real Madrid wadda ake bi bashin da ya kai kusan fan biliyan ɗaya, David Alaba kaɗai ta ɗauka a wannan kakar daga Bayern Munich kuma kyauta.

Ganin cewa Sergio Ramos da Raphael Varane waɗanda ke ɗaukar albashi mai yawa sun bar ƙungiyar, Real na ganin za ta iya sayo Mbappe ba tare da matsalar kuɗi ba.

Sai dai babu cikakken bayani kan yadda za a tsara biyan kuɗin sannan kuma har yanzu PSG ba ta ce komai kan tayin ba tukunna.

(BBCHAUSA)

More News

Ƴan Fashin Daji Sun Kashe Mutane 7 A Jihar Kebbi

Mutane 7 aka bada rahoton ƴan fashin daji sun kashe  a garin Tudun Bici dake ƙaramar hukumar Danko Wasagu ta jihar Kebbi. A cewar mazauna...

Tsoffin gwamnoni sun wawashe sama da naira tiriliyan 2 tun komawa dimokuraɗiyya

Aƙalla tsoffin gwamnoni 58 ne ake zargin sun wawure kuma sun yi almubazzarancin jimillar naira Tiriliyan 2.187 a cikin shekaru 25 tun komawa mulkin...

Ƴan sanda sun kama mutane 50 kan rikicin da ya faru a wata kasuwa a Lagos

Rundunar ƴan sandan jihar Legas ta kama mutane sama da 50 da ake zargin suna da hannu rikicin da ya faru a kasuwar Ile...

Ƴan Sanda sun kama wanda ya shirya kai harin jirgin ƙasar Abuja-Kaduna a shekarar 2022

Rundunar ƴan sandan Najeriya ta ce jami'anta sun kama wani mutum mai suna Ibrahim Abdullahi wanda ake zargi da kitsa harin jirgin ƙasar da...