Kungiyar Likitoci ta NARD Ta Dakatar Da Zanga-Zangar Da Ta Shirya Yi

Kungiyar Likitoci Masu Neman Kwarewa ta NARD ta dakatar da zanga-zangar da suka shirya yi a fadin Najeriya ranar 9 ga watan Agusta.

Wakilan gwamnatin tarayya sun gana da yan kungiyar likitocin a ranar Talata kan shirunsu na fara yajin aikin da kuma zanga-zangar.

Emeka Orji, shugaban kungiyar ya ce abun da aka cimma a wurin ganawar shi zai tabbatar ko za ayi zanga-zangar.

Orji ya fadawa jaridar The Cable cewa an dakatar da yin zanga-zangar kuma za su sake tsayar da matsaya cikin awanni 72.

Kungiyar ta yi hakan ne bayan ganawar da tayi da Godswill Akpabio shugaban majalisar dattawa da kuma wasu daga cikin jagororin majalisar.

More News

Gwamnatin Abia za ta fara biyan albashi mafi maranci na naira 70,000 a watan Oktoba

Gwamnatin Jihar Abia ta sanar da cewa za ta fara biyan sabon albashi mafi karanci na naira 70,000 ga ma’aikatanta daga watan Oktoba 2024.Kwamishinan...

Sojoji sun lalata haramtattun matatun mai 32 a yankin Neja Delta

Dakarun sojan Najeriya na runduna ta 6 dake Fatakwal sun samu nasarar lalata haramtattun matatun man fetur 32 tare da ƙwace lita 250,000 na...

An gudanar da bikin cikar Kwankwaso shekara 68.

Tarin magoya baya da kuma abokanan siyasar tsohon gwamnan jihar Kano, Sanata Rabi'u Kwankwaso ne suka halarci taron lakca da aka shirya domin bikin...

Faruk Lawan ya kammala zaman gidan yarin Kuje

An sako tsohon É—an majalisar wakilai ta tarayya, Hon Faruk Lawan daga gidan yarin Kuje bayan da ya kammala zaman gidan yarin na shekaru...