Kotun Ƙoli Ta Bada Umarnin A Cigaba Da Tsare Nnamdi Kanu

Kotun Koli ta bayar da umarnin da a cigaba da yiwa Nnamdi Kanu shariar da ake masa kan zargin aikata ta’addanci.

Alkalai biyar da suka saurari shariar sun yanke hukuncin ne a ranar Juma’a.

Kanu na tsare ne a hannun hukumar tsaro ta farin kaya DSS tun bayan da aka taso keyarsa daga kasar Kenya a ranar 19 ga watan Yuni na shekarar 2021.

Inda daga bisani gwamnatin tarayya ta gurfanar da shi a gaban kotu inda take tuhumarsa da aikata ta’addanci.

A ranar 13 ga watan Octoba ne na shekarar 2022 ne kotun ɗaukaka ta kori ƙarar da ake masa inda ta bayar da umarni da a sake shi.

A hukuncin na ranar Juma’a dukkanin alkalan biyar sun amince da soke hukuncin da kotun daukaka karar tayi.

More News

Kotu ta É—aure mutumin sa ya yi sama-da-faÉ—i da kuÉ—in marayu

Babbar kotu a jihar Borno ta yanke wa Isiyaku Ibrahim hukuncin shekara ɗaya a gidan yari da zaɓin biyan tarar naira dubu 100 saboda...

NFF ta naÉ—a Finidi George a matsayin sabon kocin Super Eagle

An naɗa Finidi George a matsayin sabon mai horar da kungiyar ƙwallon ƙafar Najeriya wato Super Eagle. Hukumar ƙwallon Ƙafa ta Najeriya, NFF ita ta...

Gwamnan Edo Zai Fara Biyan 70,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

Gwamnan jihar Edo, Godwin Obaseki ya sanar da mafi ƙarancin albashi ga ma'aikatan ga ma'aikatan jihar inda za a riƙa biyan naira dubu 70,000. Gwamnan...

JAMB ta fitar da sakamakon jarabawar 2024

Hukumar shirya jarabawar shiga makarantun gaba da sakandire ta JAMB, ta fitar da sakamakon jarrabawar shekarar 2024, watau sakamakon UTME.Sama da mutane miliyan 1.94...