Kotu ta tabbatar da Abba Kabir a matsayin dan takarar PDP a Kano

Dan takarar Kwankwasiyya Abba Kabir Yusuf

Kotu ta ce Abba Kabir Yusuf ne sahihin dan takarar gwamna a jam’iyyar PDP a jihar Kano.

Wata Kotun daukaka kara a Kaduna ce ta yi watsi da hukuncin da wata kotun tarayya a Kano ta zartar wacce ta rushe zaben da jam’iyyar PDP ta gudanar a jihar Kano wanda ya bai wa Abba Kabir Yusuf damar zama dan takarar gwamna a jam’iyyar.

Alkalin Kotun daukaka karar a Kaduna Daniel O. Kalio ya jingine hukuncin da kotun Tarayya ta zartar tare da yin umurni ga hukumar zabe INEC kada ta yi aiki da umurnin kotun Kano.

Kotun yanzu ta ba bangarorin biyu kwana biyar su gabatar da bayanai domin yin nazari kafin ta sake yin zama domin sauraren daukaka karar da bangaren Kwankwansiyya ya shigar.

  • Abba Kabir Yusuf ne muka sani dan takarar PDP a Kano – INEC
  • Yadda aka fafata muhawarar gwamnan jihar Kano

A ranar Litinin ne babbar kotun tarayya a Kano ta rushe zaben na jam’iyyar PDP.

Dan takarar gwamna a jam’iyyar ta PDP, Ali Amin-little, ne ya shigar da karar yana kalubalantar yadda aka yi zaben da har Abba Kabir Yusuf ya zama dan takara.

More News

An kashe kwamandan soji a Katsina

An kashe kwamandan sojoji na wani sansanin soji da ke Sabon Garin Dan’Ali a karamar hukumar Danmusa a jihar Katsina a wani harin kwantan...

Magoya bayan APC da dama sun koma NNPP a Kano

Jam'iyar NNPP ta karɓi magoya bayan jam'iyar APC da dama a jihar Kano. Mataimakin gwamnan jihar Kano, Aminu Abdul Salam Gwarzo shi ne ya karɓi...

APC ta dakatar da Ganduje a matakin gunduma

Mambobin jam'iyyar APC a mazabar da ke Karamar Hukumar Dawakin Tofa a Jihar Kano sun dakatar da Shugaban Jam’iyyar APC na kasa Abdullahi Ganduje. ...

Yadda rikici a kan gishirin N20 ya yi sanadiyyar mutuwar wani mutum a Kano

Wani magidanci mai suna Zakari Hamza mai shekaru 45, ya gamu da ajalinsa a hannun kanen matarsa, wani Magaji Salisu saboda gishirin N20. Dan marigayin,...