Kotu ta bayar da belin likitan da ake zargi da cirewa wata mata koɗa a Jos

Wata kotun majistire dake zamanta a Jos ta bayar da belin Noa Kekere mutumin da ake zargi da sace koɗar wata mata a garin Jos.

Yan sanda sun kama Kekere tare da wasu mutane biyu da suka taimaka masa wajen cire koɗar mutane biyu a Asibitin Murna Clinic and Maternity dake Ƴanshanu a karamar hukumar Jos North.

A yayin zaman shari’ar ranar Talata mai shari’a, Chief Majistire Joseph Chollom ya bayar da belin wanda ake zargi tare da gindaya wasu sharuɗa da suka haɗa mutane biyu da za su tsaya masa da suke da cikakkun takardar mallakar gida da kuma basaraken gargajiya guda ɗaya.

More from this stream

Recomended

Kotun Tarayya Ta Tabbatar Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC

Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta tabbatar da shugabancin jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) ƙarƙashin jagorancin tsohon shugaban majalisar dattawa, David Mark. Kotun ta yi watsi da ƙarar da ɗan majalisar wakilai, Leke Abejide, ya shigar kan shugabancin jam’iyyar, inda ta bayyana cewa lamarin ya shafi harkokin cikin gida na jam’iyyar siyasa. Mai […]