Wata kotun majistire dake zamanta a Jos ta bayar da belin Noa Kekere mutumin da ake zargi da sace koɗar wata mata a garin Jos.
Yan sanda sun kama Kekere tare da wasu mutane biyu da suka taimaka masa wajen cire koɗar mutane biyu a Asibitin Murna Clinic and Maternity dake Ƴanshanu a karamar hukumar Jos North.
A yayin zaman shari’ar ranar Talata mai shari’a, Chief Majistire Joseph Chollom ya bayar da belin wanda ake zargi tare da gindaya wasu sharuɗa da suka haɗa mutane biyu da za su tsaya masa da suke da cikakkun takardar mallakar gida da kuma basaraken gargajiya guda ɗaya.