Kamfanonin sadarwa na duba yiyuwar ƙara kuɗin kira da data

Kungiyar kamfanonin da suke da lasisin samar da kamfanonin sadarwa a Najeriya(ALTON) ta ce kuɗin da ake cajin masu amfani da wayar salula a yanzu ba abu ne da zai dore ba a halin da ake ciki yanzu.

Shugaban kungiyar Gbenga Adebayo shi ne ya bayyana haka a wurin taron masu ruwa da tsaki a harkar sadarwa da shugaban hukumar sadarwa ta kasa NCC, Dr Aminu Maida.

Ya ce ya kamata a duba farashin dai-dai yadda ake samun karuwar kuɗin da suke kashewa wajen gudanar da ayyukansu inda ya kara da cewa masu kamfanonin andora musu nauyin biyan haraji har kusan guda 52.

More from this stream

Recomended