Juyin mulki: Najeriya ta rufe iyakokinta da Nijar

A ranar Juma’ar ne gwamnatin tarayyar Najeriya ta ba da umarnin rufe dukkan iyakokin kasar da jamhuriyar Nijar cikin gaggawa sakamakon juyin mulkin da aka yi a baya-bayan nan da kuma tashe-tashen hankulan siyasa da ake fama da su a kasar.

A cewar Bashir Adeniyi Adewale, mukaddashin Kwanturola-Janar na Hukumar Kwastam ta Najeriya (NCoS), wannan mataki na da matukar amfani ga kasashen biyu.

Gwamnatin tarayya ta umurci masu ruwa da tsaki kan harkokin kula da kan iyakokin kasar da su bada tabbacin cikakken bin wannan umurni, a cewar Adewale, wanda ya je kan iyakar Jibia a jihar Katsina domin sa ido kan matakin da aka dauka.

An ambato Mista Adeniyi yana cewa, “Kamar yadda muka sani, shugaban kasa Ahmed Bola Tinubu ya kasance mai fafutukar hada kan tattalin arziki a yammacin Afirka. Ya yi imanin cewa kasuwanci da makwabtanmu zai iya kawo ci gaba ga ‘yan Najeriya da sauran jama’ar yankin.”

More News

Ƴansanda sun kama muggan ƴan fashi da makami

Jami’an hukumar ‘yan sanda reshen Elemoro reshen jihar Legas sun kama wasu mutane uku da ake zargi da hannu a fashi da makami a...

An kama wasu mutane biyu da hodar ibilis a Lagos

Rundunar ƴan sandan jihar Lagos ta sanar da kama wasu mutane biyu da aka samu ɗauke da ƙunshin hodar ibilis mai yawan gaske. Mai magana...

Ƴan sanda sun kama wani mutum ɗauke da bindigogi 20 a Kaduna

Rundunar ƴan sandan jihar Kaduna ta ce jami'anta sun kama wani  riƙaƙƙen mai safarar bindiga inda aka same shi da bindigogin AK-47 ƙirar gida...

Kwankwaso ya bada tallafin miliyan ₦50 ga mutanen da ambaliyar Borno ta shafa

Tsohon gwamnan jihar Kano kuma jagoran jam'iyar NNPP, Sanata Rabi'u Musa Kwankwaso ya bada tallafin naira miliyan 50 ga mutanen da ambaliyar ruwa a...