Juyin mulki: An yanke alaƙar difulomasiyya tsakanin Nijar da Najeriya

Gwamnatin mulkin soja a Jamhuriyar Nijar ta yanke hulda da Najeriya bayan kokarin da kungiyar raya tattalin arzikin kasashen yammacin Afirka ECOWAS ta yi na warware rikicin shugabancin da kasar ke fama da shi.

An ruwaito cewa kungiyar ECOWAS ta bayar da wa’adin kwanaki bakwai ga gwamnatin mulkin soja ta mayar da hambararren shugaban kasar Mohamed Bazoum kan kujerarsa.

A ranar Alhamis ne shugaban Najeriya Bola Tinubu ya aike da wata tawaga mai karfi zuwa kasar domin ganawa da wadanda suka yi juyin mulki.

Sai dai jaridar Daily Trust ta ruwaito cewa tawagar karkashin jagorancin Janar Abdulsalami Abubakar (rtd) ta gana da wakilan gwamnatin mulkin soja ne kawai, inda ta kara da cewa Nijar ta yanke hulda da Najeriya da Togo da Faransa da kuma Amurka.

“An kawo karshen ayyukan manyan jakadun Jamhuriyar Nijar” a kasashen Faransa da Najeriya da Togo da kuma Amurka,” in ji jaridar Rediyo Faransa ta nakalto daya daga cikin wadanda suka yi juyin mulkin a gidan talabijin na kasar.

More News

Ƴan sanda sun kama mutane 50 kan rikicin da ya faru a wata kasuwa a Lagos

Rundunar ƴan sandan jihar Legas ta kama mutane sama da 50 da ake zargin suna da hannu rikicin da ya faru a kasuwar Ile...

Ƴan Sanda sun kama wanda ya shirya kai harin jirgin ƙasar Abuja-Kaduna a shekarar 2022

Rundunar ƴan sandan Najeriya ta ce jami'anta sun kama wani mutum mai suna Ibrahim Abdullahi wanda ake zargi da kitsa harin jirgin ƙasar da...

Sojoji Sun Ceto Mutane Daga Hannun Masu Garkuwa Da Mutane A Filato

Dakarun rundunar Operation Safe Haven dake aikin tabbatar da tsaro a jihar Filato da wani ɓangare na jihar Kaduna sun samu nasarar ceto mutane...

Matatar Mai Ta Kaduna Za Ta Fara Aiki A Ƙarshen 2024

Kamfanin Kaduna Refining and Petrochemical Company KPRC ya ce matatar mansa za ta fara aiki a shekarar 2024. Mustapha Sugungun managan matatar man ta KRPC...