Jirgin ƙasar Abuja zuwa Kaduna ya kauce daga kan digarsa a Abuja

Fasinjoji da dama ne suka yi carkwo-carkwo bayan da jirgin ƙasa da ya tashi daga Abuja zuwa Kaduna ya sauka daga kan digarsa a tashar Asha dake birnin tarayya Abuja.

Ɗaya daga cikin fasinjojin dake cikin jirgin ya faɗawa jaridar The Cable cewa jirgin ya kauce daga kan digarsa ne da misalin ƙarfe 03:30 na rana ƙasa da mintuna 30 bayan da ya bar tashar Kubwa.

“Fasinjoji sun yi carkwo-carkwo suna zaman jira kuma babu alamun zuwan hukumomi da aka sanarwa da faruwar lamarin,”

Wannan ne karon na biyu cikin makonni biyu da jirgin ƙasar ya ke sauka daga kan layinsa.

A ranar 26 ga watan Mayu jirgin ya kauce daga kan layinsa  bayan da ya baro tashar Rigasa dake Kaduna akan hanyarsa ta zuwa Abuja.

Tarago uku ne ya sauka daga kan digar jirgin amma babu  mutanen da suka jikkata.

More News

Mai magana da yawun Tinubu ya ajiye aikinsa na wani lokaci

Mai ba shugaban kasa shawara na musamman kan harkokin yada labarai Ajuri Ngelale ya ajiye aikinsa na wani lokaci domin tunkarar matsalar lafiya.Mista Ngelale...

Ali Jita ya koma jam’iyar APC daga NNPP

Mataimakin shugaban majalisar dattawa dattawa, Sanata Barau Jibrin ya karɓi fitaccen mawakin Kannywood, Aliyu Isa Jita daga jam'iyar NNPP ya zuwa jam'iyar APC. Ali Jita...

An yi jana’izar mutumin da ya ƙirƙiri tutar Najeriya

Iyalan marigayi, Pa Taiwo Akinkumi mutumin da ya ƙirƙiro tutar Najeriya sun yi bikin binne shi bayan da gwamnatin tarayya ta gaza cika alƙawarin...

‘Za a ƙara wa ƴan bautar ƙasa na NYSC alawus’

Babban daraktan hukumar yi wa kasa hidima ta kasa (NYSC) Birgediya Janar Yushau Ahmed, ya tabbatar wa ‘yan bautar kasar cewa za a kara...