Jiragen kamfanin Nigeria Air ya fara aiki

Rahotanni sun bayyana cewa wani jirgin kamfanin Nigeria Air, mai jigilar kayayyaki a Najeriya, ya kaddamar da tashinsa na farko zuwa filin jirgin saman Nnamdi Azikiwe da ke babban birnin Najeriya, Abuja.

A halin yanzu dai jirgin ya bar birnin Addis Ababa na kasar Habasha, kuma ya isa birnin Abuja.

Tun da farko dai, jaridar Daily Trust ta ruwaito cewa alkawarin da kamfanin dillalan jiragen ya yi na fara aiki kafin wa’adin shugaban kasa Muhammadu Buhari ya kare a ranar 29 ga watan Mayu bai cika ba.

Sai dai a martanin da ya mayar kan rahoton, ministan sufurin jiragen sama, Hadi Sirika, ya tabbatar da cewa, kamfanin na Najeriya Air zai fara aiki a cikin wa’adin da aka kayyade.

More News

An Jikkata Jami’an Tsaro A Harin Da Ƴan Bindiga Su ka Kai Wa Ayarin Motocin Yahaya Bello

A jikkata wasu jami'an tsaro a wani hari da yan bindiga su ka kai kan jerin ayarin motocin gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello ranar...

Bala Muhammad ya zama shugaban gwamnonin jam’iyyar PDP

An zaɓi gwamnan jihar Bauchi, Bala Muhammad a matsayin sabon shugaban kungiyar gwamnonin jam'iyyar PDP. Siminalayi Fabura zaɓaɓɓen gwamnan jihar Rivers shi ne mataimakin shugaban...

Za mu sake bitar mafi karancin albashi a Najeriya—Tinubu

Shugaba Bola Tinubu ya yi alkawarin sake nazarin mafi karancin albashin ma’aikata domin dacewa da yanayin tattalin arzikin kasar nan. A cewarsa, akwai bukatar...

EFCC na zargin tsohuwar ministar mata a mulkin Buhari da karkatar da naira biliyan 2

Hukumar EFCC dake yaƙi da masu yiwa tattalin arzikin kasa ta'annati ta titsiye tsohuwar ministar harkokin mata Pauline Tallen kan zargin azurta kai ta...