Jiragen kamfanin Nigeria Air ya fara aiki

Rahotanni sun bayyana cewa wani jirgin kamfanin Nigeria Air, mai jigilar kayayyaki a Najeriya, ya kaddamar da tashinsa na farko zuwa filin jirgin saman Nnamdi Azikiwe da ke babban birnin Najeriya, Abuja.

A halin yanzu dai jirgin ya bar birnin Addis Ababa na kasar Habasha, kuma ya isa birnin Abuja.

Tun da farko dai, jaridar Daily Trust ta ruwaito cewa alkawarin da kamfanin dillalan jiragen ya yi na fara aiki kafin wa’adin shugaban kasa Muhammadu Buhari ya kare a ranar 29 ga watan Mayu bai cika ba.

Sai dai a martanin da ya mayar kan rahoton, ministan sufurin jiragen sama, Hadi Sirika, ya tabbatar da cewa, kamfanin na Najeriya Air zai fara aiki a cikin wa’adin da aka kayyade.

More from this stream

Recomended

Trump Ya Yaba Wa Tinubu Kan YaÆ™i Da Ta’addanci A Najeriya

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya yaba wa Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, kan abin da ya bayyana a matsayin Æ™wazon jagorancinsa wajen yaÆ™i da ta’addanci da magance matsalar tsaro a Æ™asar. A cewar Fadar Shugaban Ƙasa, Trump ya bayyana hakan ne cikin wata wasiÆ™a da ya aike wa Tinubu. Ya ce yana yaba wa shugaban […]