Jiragen ƙasa za su fara aiki da daddare a Najeriya

Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen kasa ta Najeriya ta kammala shirin fara gudanar da ayyukan dare kafin karahen watan shida na shekarar 2024.

Manajan Darakta na NRC, Fidet Okhiria, ne ya bayyana hakan yayin wata tattaunawa da kamfanin dillancin labarai na Najeriya a ranar Litinin.

Ya fara da cewa, “Abin da ya takaita mana ayyukanmu shi ne aikin dare, kuma ba haka ya kamata jiragen kasa su rika aiki ba. Jirgi ana so yana aiki ne a kowane lokaci. Mutane na iya son yin tafiye-tafiye da yamma, amma saboda yanayin tsaro a kasar, sai mu takaita da rana.

“Muna da niyyar dawo da fasinja da jiragen dakon kaya daga Fatakwal zuwa Aba, Legas zuwa Kano, da kuma Kaduna saboda tashoshi kan tudu,” in ji Okhiria.

More News

An kashe kwamandan soji a Katsina

An kashe kwamandan sojoji na wani sansanin soji da ke Sabon Garin Dan’Ali a karamar hukumar Danmusa a jihar Katsina a wani harin kwantan...

Gwamantin Kano na kashe naira biliyan 1.2 duk wata don samar da ruwan sha—Kwamishina

Gwamnatin jihar Kano na kashe kimanin naira biliyan 1.2 duk wata don samar da ruwan sha na tafi da gidanka a cikin babban birnin...

Magoya bayan APC da dama sun koma NNPP a Kano

Jam'iyar NNPP ta karɓi magoya bayan jam'iyar APC da dama a jihar Kano. Mataimakin gwamnan jihar Kano, Aminu Abdul Salam Gwarzo shi ne ya karɓi...

APC ta dakatar da Ganduje a matakin gunduma

Mambobin jam'iyyar APC a mazabar da ke Karamar Hukumar Dawakin Tofa a Jihar Kano sun dakatar da Shugaban Jam’iyyar APC na kasa Abdullahi Ganduje. ...