Gwamnatin jihar Yobe ta ce ta shirya gudanar da zaben kananan hukumomi a ranar 25 ga watan Nuwamba 2023.
Sakataren gwamnatin Jihar, Baba Mallam Wali shi ne ya bayyana haka cikin wata wasika da ya aikewa Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta Ta Jihar Yobe.
Wali ya aike da wasikar ne biyo bayan amincewar da gwamnan jihar, Mai Mala Buni ya yi na gudanar da zaben.
Gwamna Buni ya rushe shugabancin ƙananan hukumomin jihar biyo bayan karewar wa’adinsu.