Jam’iyun Habasha za su yi maja

Prime Minister Abiy Ahmed says the new party would help reduce ethnic divisions in Ethiopia

Hakkin mallakar hoto
Reuters

‘Yan siyasa a jam’iyya mai mulkin kasar Habasha ta People’s Revolutionary Democratic Front sun amince da wani shiri na kafa wata sabuwar jam’iyyar siyasa

Firai minista Abiy Ahmed ya fito yana mara wa wannan matakin na ‘yan siyasar baya.

Mista Abiy ya ce jam’iyyar da aka sanya wa suna Ethiopian Prosperity Party za ta taimaka wajen hada kan kabilun kasar wuri guda, kuma za ta hada kan ‘yan kasar.

Yana son sabuwar jam’iyyar ta zama wata hanya da za ta jagoranci siyasar kasar a madadin tsarin da aka shafe shekaru 30 ana bi na jam’iyyu masu alaka da manyan kabilun kasar.

Amma wani dan siyasa daa jam’iyyar Tigray People’s Liberation Front, jam’iyyar da ta mamaye siyasar kasar kafin zuwan Mista Abiy ya ce ba zai shiga sabuwar jam’iyyar ba.

Ya ce dalilinsa shi ne, shiga sabuwar jam’iyyar na iya dakushe karfin fada aji na bangaren siyasa da yake wakilta.

Firai minista Abiy ya aika da wani sako na Twitter, wanda a ciki ya ke cewa majar “wani muhimmin mataki ne a kokarinmu na hada karfinmu wuri guda domin cimma makomar da muke bukatar ganin kasarmu ta cimma.”

[ad_2]

More News

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma’aikatar kudin jihar ta miÆ™ata bayanan bashin da El-Rufai ya ciwo

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma'aikatar kudi ta jihar da ta miƙa mata cikakken bayani kan basukan  da gwamnatin tsohon gwamnan jihar, Nasiru...

An dakatar da ayyukan kamfanin jiragen sama na Dana Air

Festus Keyamo, ministan harkokin sufurin jiragen sama ya umarci hukumar FAAN dake lura da sufurin jiragen sama a Najeriya ta dakatar da ayyukan kamfanin...

Yahaya Bello Ya Bayyana Dalilan Da Ya Hana Shi Bayyana A Gaban Kotu

Tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello ya ce tsoron kamun  hukumar EFCC dake yaÆ™i da yiwa tattalin arzikin Æ™asa ne ya hana shi bayyana...

Ƴan sanda sun kama mutane biyu dake samarwa ƴan fashin daji makamai a jihar Kaduna

Rundunar Æ´an sandan jihar Kaduna ta ce tana tsare da wasu mutane biyu da ake zargi da safarar bindiga a jihar. A wata sanarwa ranar...