Jami’an Tsaro Sun Yi Wa Masallacin Ashabul Khafi Kawanya

VOA Hausa
Hakan na zuwa ne kasa da sa’o’I 24 da umarnin gwamnatin jihar Kano wadda ke haramtawa Malamin gudanar da wa’azi karantarwar a wurin da-ma kowane wuri a fadin jihar saboda zarginsa da kalaman tunzura Jama’a da ka iya barazana ga zaman lafiya a jihar.
A cikin wata sanarwa, kwamishinan labarun gwamnatin Kanon, Comrade Mohammed Garba yace, majalisar zartarwa jihar ta kuma umarci kafofin yada labarai a fadin jihar su daina saka muryar Malamin a dukkanin shirye shiryen su domin tabbatar da doka da oda a tsakanin al’umar jihar.
Bayanai daga majiyoyin tsaro a Kano na nuni da cewa, Sheikh Abduljabbar din ya yi wata ganawa da makusanta da almajiran sa game da yanayin da aka tsinci kai. Sai dai babu wani bayani dangane da sakamakon tattaunawar ta su.
takaddama-tsakanin-kungiyoyi-da-gwamnatin-jihar-kano-kan-wuraren-ibada
shawarar-ganduje-kan-makiyaya-ta-saba-doka-bulama-bukarti
A hannu guda kuma, wasu mabiya darikar shi’a sun gudanar da wata kwarkwaryar zanga zanga domin nuna goyon bayan su ga Malamin. Sai dai cikin sauri ‘yan sanda suka tarwatsa masu zanga zangar jim kadan bayan sun fara yin gangami a kusa da asibitin Murtala dake cikin birnin Kano.
Yanzu haka dai gwamnatin jihar ta kafa kwamitin bincike kan yadda Malamin ke gudanar da harkokin sa. Kwamitin dai ya kunshi Jami’an tsaro da Malamai da kuma Jami’an gwamnati. Ana sa ran rahotan kwamitin ne zai baiwa gwamnati alkibilar mataki na gaba game da wannan batu.

Wakilan majalissar malaman Sunna Kano
Wakilan majalissar malaman Sunna Kano

A martanin sa ga matakin na gwamnati, Sheikh Abduljabbar Nasiru Kabara ya alakanta lamarin da cewa, siyasa ce kawai, domin kuwa a cewarsa,yana cikin wadanda ba su goyi bayan gwamnatin Abudllahi Umar Ganduje ba. A don haka sai ya bukace almajiran sa da sauran mabiya da su dauki damarar zabar gwamnatin da zata ba su sukunin gudanar da addininsu yadda ya kamata a nan gaba.
Wannan lamarin ya ja hankalin wadansu masu sharhi a shafukan zumunta
Wakilinmu dake Kano ya ruwaito cewa, Jama’a a birni da kewayan Kano na ci gaba da gudanar da harkokin su na yau da kullum yadda ya kamata.

More News

Ƴan Fashin Daji Sun Kashe Mutane 7 A Jihar Kebbi

Mutane 7 aka bada rahoton ƴan fashin daji sun kashe  a garin Tudun Bici dake ƙaramar hukumar Danko Wasagu ta jihar Kebbi. A cewar mazauna...

Tsoffin gwamnoni sun wawashe sama da naira tiriliyan 2 tun komawa dimokuraÉ—iyya

Aƙalla tsoffin gwamnoni 58 ne ake zargin sun wawure kuma sun yi almubazzarancin jimillar naira Tiriliyan 2.187 a cikin shekaru 25 tun komawa mulkin...

Ƴan sanda sun kama mutane 50 kan rikicin da ya faru a wata kasuwa a Lagos

Rundunar Æ´an sandan jihar Legas ta kama mutane sama da 50 da ake zargin suna da hannu rikicin da ya faru a kasuwar Ile...

Ƴan Sanda sun kama wanda ya shirya kai harin jirgin ƙasar Abuja-Kaduna a shekarar 2022

Rundunar ƴan sandan Najeriya ta ce jami'anta sun kama wani mutum mai suna Ibrahim Abdullahi wanda ake zargi da kitsa harin jirgin ƙasar da...