Jami’an Tsaro Sun Ceto Mutane 21 Da Aka Yi Garkuwa Dasu A Jihar Kogi

Jami’an tsaro a jihar Kogi sun samu nasarar ceto wasu mutane 21 sa’o’i 48 bayan anyi garkuwa da su.

Gwamna Yahaya Bello wanda ya yabawa kokarin jami’an tsaron ya jaddada cewa babu jihar baza ta amince da] masu aikata laifi.

A wata sanarwa da mai taimakawa gwamnan kan kafafen yaÉ—a labarai Onogwu Muhammad ya fitar ta ce hadin gwiwar jami’an tsaron Æ´an sanda, Civil Defence da kuma yan bijilante ne suka samu nasarar ceto mutanen.

Mutanen da aka ceto da yawancinsu matafiya ne anyi awon gaba da su ne a wajen wani daji mai sarkakiya dake karamar hukumar Ajaokuta ta jihar.

Muhammad ya ce samun labarin sace mutanen ke da wuya gwamna Bello ya bawa jami’an tsaro da kuma yan bijilante umarnin yin duk mai yiwuwa wajen ganin an ceto mutanen tare da kama wadanda suka yi garkuwat da su.

Wasu daga cikin masu garkuwar sun fada hannun jami’an tsaro a yayin da wasu suka tsere da raunin harbin bindiga kuma jami’an tsaron na cigaba da bibiyarsu.

More News

Ƴan sanda sun kama mutane 50 kan rikicin da ya faru a wata kasuwa a Lagos

Rundunar Æ´an sandan jihar Legas ta kama mutane sama da 50 da ake zargin suna da hannu rikicin da ya faru a kasuwar Ile...

Ƴan Sanda sun kama wanda ya shirya kai harin jirgin ƙasar Abuja-Kaduna a shekarar 2022

Rundunar ƴan sandan Najeriya ta ce jami'anta sun kama wani mutum mai suna Ibrahim Abdullahi wanda ake zargi da kitsa harin jirgin ƙasar da...

Sojoji Sun Ceto Mutane Daga Hannun Masu Garkuwa Da Mutane A Filato

Dakarun rundunar Operation Safe Haven dake aikin tabbatar da tsaro a jihar Filato da wani É“angare na jihar Kaduna sun samu nasarar ceto mutane...

Matatar Mai Ta Kaduna Za Ta Fara Aiki A Ƙarshen 2024

Kamfanin Kaduna Refining and Petrochemical Company KPRC ya ce matatar mansa za ta fara aiki a shekarar 2024. Mustapha Sugungun managan matatar man ta KRPC...