Rundunar tsaron haɗin gwiwa ta Operation Hadarin Daji dake kai ɗaukin gaggawa a yankin arewa maso yamma dake Malekachi a jihar Kebbi ta samu nasarar ceto wani ɗan sanda da kuma wasu mutane 16 daga hannun masu garkuwa da mutane.
Har ila yau rundunar ta samu nasarar kama babura da dama na yan bindigar a yayin da ta kai farmakin kuɓutar da mutanen.
Wata sanarwa mai ɗauke da sa hannun Yahaya Ibrahim a madadin jami’in yaɗa labarai na rundunar Operation Hadarin Daji ta ce sojojin sun hanzarta tattaruwa inda suka yi kwanton ɓauna a hanyar da suke tunanin yan bindigar za su wuce a ƙauyen Karenban.
Karfin wutar sojoji ne yasa yan bindigar suka tsere tare da barin mutanen da suke ɗauke da su.
“mutanen da aka ceto sun haɗa da mata 6 da kuma maza 11 ciki har da ɗan sanda da aka yi garkuwa da shi a Danko-Wasagu.” a cewar sanarwar.s
Sanarwar ta kara da cewa tuni aka miƙa wadanda aka ceto ga DPO yan sanda na Bena domin sada su da iyalinsu.