Ɗalibai 9 aka tabbatar da yin garkuwa da su daga jami’an jihar Kogi

Gwamnatin jihar Kogi ta tabbatar da cewa ɗalibai 9 aka tabbatar sun ɓace bayan da wasu ƴan bindiga suka kai farmaki Jami’ar Kimiya da Fasaha ta Confluence dake Osara a jihar.

Ƴan bindigar sun farma jami’ar da misalin ƙarfe 9 na daren ranar Alhamis inda suka yi awon gaba da wasu ɗalibai da ke karatun jarrabawa.

Kingsley Fanwo, kwamishinan yaɗa labarai na jihar Kogi ya faɗawa manema labarai ranar Juma’a cewa gwamnatin jihar ta tura da jami’an tsaro da kuma ɗaruruwan ƴan bijilante ya zuwa dazukan jihar domin farautar masu garkuwar.

Ya ƙara da cewa an kuma tura ƙarin jami’an tsaro ya zuwa jami’ar.

“Ɗaruruwan mafarauta wanda suka san yanayin  dazukan yankin da kuma sauran jami’an tsaro yanzu haka suna  bincike a yankin domin tabbatar da an ceto ɗaliban  da aka yi garkuwa lafiya daga ajujuwansu,” a cewar Fanwo.

“Kawo yanzu ɗalibai 9 aka tabbatar da rahoton sun ɓace  muna fatan ceto su nan ba da jimawa.”

More News

An sanar da zaman makoki na kwana biyar saboda mutuwar shugaban kasa a Iran

Jagoran juyin juya halin Musulunci na Iran Ayatollah Ali Khamenei ya sanar da zaman makoki na kwanaki biyar saboda rasuwar shugaban kasar Ibrahim Raisi...

Najeriya za ta dena shigo da man fetur a cikin watan Yuni – Dangote

Aliko Dangote mutumin da ya fi kowa arziki a Nahiyar Afirka ya ce Najeriya za ta daina shigo da man fetur a cikin watan...

An ceto mutane 9 daga wani ginin bene da ya ruguzo a jihar Niger

Mutane 9 aka samu nasarar cetowa daga wani ginin bene mai hawa ɗaya da ya ruguzo a yankin Sabon Gwari dake garin Minna babban...

An yi faɗa tsakanin masu sayar da waya da sojoji a kasuwar Abuja

Rundunar ‘yan sandan babban birnin tarayya, ta tura jami’an leken asiri zuwa kasuwar Banex – wata kasuwar kayan lantarki da na’urorin sadarwa da ke...