Hukumar NMDPRA ta rufe wani gidan mai da ya karkatar da tankar man fetur 18

Hukumar NMDPRA dake lura da tacewa tare rarraba man fetur da iskar gas ta rufe gidan man Botoson Oil and Gas LTD dake jihar Taraba.

A cikin wata sanarwa hukumar ta NMDPRA ta ce ta rufe gidan man ne bayan da aka same shi da karkatar da mota 18 ta man fetur ya zuwa kasuwar bayan fage.

Dukkanin man fetur da aka tura gidan man daga ranar 4 ga watan Afrilu ya zuwa ranar 5 ga watan Mayu bai samu isa gidan man ba ma’ana dai ya yi É“atan dabo.

Gidan man na Botoson Oil and Gas na  garin Mararaba Baisa dake Æ™aramar hukumar Kurmi ta jihar Taraba.

Rufe gidan man na zuwa ne dai-dai lokacin da ake cigaba da samun tsada da kuma dogayen layukan mai a sassa daban-daban na ƙasarnan.

More News

Zanga-zanga: An jibge Æ´an sanda 4200 a Abuja

Rundunar Æ´an sandan birnin tarayya Abuja ta tura Æ´an sanda 4200 gabanin zanga-zangar da za a gudanar a cikin watan Agusta. Kamar yadda masu shirya...

Kamfanin NNPC ya shirya daukar karin ma’aikata

Kamfanin mai na Nigerian National Petroleum Company Limited ya shirya daukar karin ma’aikata.Kakakin kamfanin na NNPC, Olufemi Soneye, ya tabbatar da hakan a wata...

Ya kamata matasa su yi haÆ™uri zanga-zanga ba ita ce mafita ba – Sarkin Zazzau

Sarkin Zazzau, Mai Martaba Ahmed Nuhu Bamalli ya ce matasa su ƙara haƙuri da gwamnatin tarayya su janye zanga-zangar da suka shirya gudanarwa a...

Zanga-zanga: Tinubu ya gana da gwamnonin APC

Shugaban ƙasa, Bola Ahmad Tinubu ya gana da gwamnonin da aka zaɓa ƙarƙashin jam'iyar APC. Taron ganawar da aka gudanar a fadar shugaban ƙasa ta...