
Jami’an hukumar EFCC dake yaki da yiwa tattalin arzikin ƙasa ta’annati sun ziyarci hedkwatar rukunin kamfanonin Dangote a jihar Lagos a yayin da hukumar ta EFCC ke faɗaɗa bincike kan batun zargin badakalar musayar kudaden waje a lokacin, Godwin Emefiele tsohon gwamnan Babban Bankin Najeriya CBN.
Idan za a iya tunawa a cikin watan Nuwamba ne Rukunin Kamfanonin Dangote ya musalta zargin cewa ya aikata ha’inci da kuma almundahanar kudade har na kusan dala biliyan 3.4.
Amma kuma ranar Alhamis hukumar EFCC ta bukaci kamfanin ya bata takardun bayanai dake da alaka da batun bawa kamfanin musayar kudaden kasar waje tun daga shekarar 2015 har ya zuwa lokacin da shugaban ƙasa, Bola Ahmad Tinubu ya dakatar da Emefiele daga kan muƙaminsa.
Wasu daga cikin ma’aikatan kamfanin sun tabbatarwa da jaridar Daily Trust cewa lallai jami’an hukumar ta EFCC sun ziyarci kamfanin.
Binciken na hukumar EFCC ba iya kamfanin Dangote ya tsaya ba ya hada da wasu manyan kamfanoni da suma suka samu musayar kudaden waje a farashin gwamnati a hannun CBN har ya zuwa shekarar 2023.