Jami’ai 4 na hukumar lura da shige da fice ta Najeriya sun mutu a hatsarin mota a Kano

Hukumar Kula Da Shige Da Fice ta Najeriya ta ce jami’anta huɗu sun mutu a yayin da wasu 7 kuma suka samu rauni a wani hatsarin mota akan hanyar Kano-Zaria.

Hatsarin ya faru ne ƴan kilomitoci kaɗan daga birnin Kano.

Mai magana da yawun hukumar, Adedotun Aridegbe shi ne ya sanar da faruwar lamarin a wurin wani taron manema labarai ranar Litinin a Abuja.

Aridegbe ya ce ma’aikatan na kan hanyarsu ne ta komawa Abuja daga wani aiki da aka tura su a Kano a lokacin da lamarin ya faru.

Ya kara da cewa awadanda suka samu rauni a hatsarin na samun kulawa a Asibitin Koyarwa na Mallam Aminu Kano dake Kano.

More from this stream

Recomended