Hukumar zaɓe mai zaman kanta ta kasa, INEC ta musalta maganar da ake yadawa cewa ta janye daga daukaka kara kan shari’ar zaɓen jihar Kano.
Hukumar ta bayyana haka ne cikin wata sanarwa da ta fitar ranar Asabar.
Sanarwar ta ce babu inda aka umarci wani jami’i ya rubuta takardar janye ƙara kuma tuni aka janye waccen takarda tare da daukar mataki kan jami’in da ya rubuta takardar.
A jiya ne dai wata takarda ta bulla mai dauke da sahannin jami’in sashen shari’a na ofishin INEC na Kano dake cewa hukumar ta janye daga shari’ar.
Sanarwar t ta shawarci jama’a da su yi watsi da abun da waccan takarda ta ƙunsa.