Hukumar hana shan ƙwayoyi a Najeriya ta gano kamfanin hada A-kurkura a Adamawa

Hukumar ta ce kamfanin ya gawurta domin har yana fitar da A-kuskura zuwa kasashen Chadi da Kamaru da Jamhuriyyar Nijar.


A kwanakin baya ne NDLEA ta yi gargadi kan amfani da A-kuskura. Photo/NDLEA
Hukumar da ke yaki da sha da fataucin miyagun kwayoyin a Nijeriya NDLEA ta ce ta gano wani kamfani da ake hada A-kuskura a garin Mubi na Jihar Adamawa.

Hukumar ta ce kamfanin ya gawurta domin har yana fitar da A-kuskura zuwa kasashen Chadi da Kamaru da Jamhuriyyar Nijar.

Mai magana da yawun hukumar ta NDLEA Femi Babafemi ne ya sanar da batun kamun a wata sanarwa da ya fitar mai kunshe da bayanai kan kamen da suka yi na miyagun kwayoyi.

Babafemi ya bayyana cewa a lokacin da da aka kai samamen, ana cikin aikin hada A-kuskura.

A-kuskura dai wani hadi ne ko kuma jiko da ke sa mutum maye ko kuma ya fita daga cikin hayyacinsa musamman a karon farko da aka soma amfani da shi.

More News

Najeriya za ta dena shigo da man fetur a cikin watan Yuni – Dangote

Aliko Dangote mutumin da ya fi kowa arziki a Nahiyar Afirka ya ce Najeriya za ta daina shigo da man fetur a cikin watan...

An ceto mutane 9 daga wani ginin bene da ya ruguzo a jihar Niger

Mutane 9 aka samu nasarar cetowa daga wani ginin bene mai hawa ɗaya da ya ruguzo a yankin Sabon Gwari dake garin Minna babban...

An yi faɗa tsakanin masu sayar da waya da sojoji a kasuwar Abuja

Rundunar ‘yan sandan babban birnin tarayya, ta tura jami’an leken asiri zuwa kasuwar Banex – wata kasuwar kayan lantarki da na’urorin sadarwa da ke...

Yawan Mutanen Da Suka Mutu A Wutar Da Wani Matashi Ya Cinnawa Wani Masallaci A Kano Sun  Karu Zuwa 16

Rundunar ƴan sandan jihar Kano ta ce yawan mutanen da suka mutu sakamakon wutar da wani ya cinnawa wani masallaci a ƙauyen Gadan a...