Hukumar DSS tal gurfanar da Emefiele a gaban kotu

Hukumar tsaro ta farin kaya wato DSS ta ce ta gurfanar da tsohon shugaban Babban Bankin Najeriya CBN, Godwin Emefiele a gaban kotu.

Hukumar ta sanar da haka ne a matsayin wani martani da umarnin da babbar kotun birnin tarayya dake cewa a saki Emefiele cikin kwana bakwai ko kuma a gurfanar da shi a gaban kotu.

Alkalin kotun mai shari’a Hamza Mu’azu shi ne ya yanke hukuncin kan kara da Emefiele ya shigar na tauye masa hankinsa na dan adam.

Kakakin hukumar ta DSS, Peter Afunaya a cikin wata sanarwa da ya fitar ya ce tuni hukumar ta bi umarnin kotun ta hanyar gurfanar da Emefiele a gaban kotu.

Afunaya ya tabbatarwa da jama’a cewa hukumar za ta cigaba da nuna kwarewa, adalci da kuma dai-daito a wajen binciken tare da yin ayyukanta bisa bin doka.

More News

Tinubu Ya Dawo Abuja Daga Ziyarar Aiki Da Ya Kai  Saudiya da Nezaland

Shugaban ƙasa, Bola Ahmad Tinubu ya dawo Abuja bayan ziyarar aiki da ya kai ƙasashen Saudiya da Nezaland. A ranar 22 ga watan Afrilu ne...

CBN ya dakatar da kudirinsa na sa bankuna su riƙa cajar kwastomominsu

Babban bankin Najeriya ya umarci bankunan da su dakatar da cajin kudaden ajiya har zuwa ranar 30 ga Satumba, 2024.Babban bankin ya bayyana hakan...

Ƴansanda sun kama likitan bogi

Rundunar ‘yan sanda ta Zone 2, Onikan, Legas, ta kama wani likitan jabu mai shekaru 37, kuma ma’aikacin lafiya, tare da zargin amfani da...

Gwamnan Kano ya sanya hannu kan dokar yin gwajin lafiya kafin aure

Gwamnan jihar Kano, Engr Abba Kabir Yusuf ya sanya hannu kan wata doka za ta tilastawa masu yin aure yin wasu gwaje-gwajen lafiya gabanin...