Har yanzu jihohin Bauchi da Zamfara ba su karbi shinkafarsu daga gwamnatin tarayya ba

Jihohin Bauchi da Zamfara dai har yanzu ba su samu tirelolin shinkafar da gwamnatin tarayya ta yi alkawari ga daukacin jihohin ba a matsayin wani mataki na rage radadin rashin abinci da ake fama da shi.

Sai dai jihar Bayelsa ta karbi tirela 20 na shinkafar daga gwamnatin tarayya domin rabawa dukkanin kananan hukumomin jihar nan take.

Wani babban mataimaki na musamman kan harkokin yada labarai da sadarwa ga gwamna Dauda Lawal na jihar Zamfara, Mustafa Jafaru, ya bayyana cewa har yanzu gwamnatin jihar ba ta karbi shinkafar ba har zuwa lokacin hada wannan rahoto.

More News

Mai magana da yawun Tinubu ya ajiye aikinsa na wani lokaci

Mai ba shugaban kasa shawara na musamman kan harkokin yada labarai Ajuri Ngelale ya ajiye aikinsa na wani lokaci domin tunkarar matsalar lafiya.Mista Ngelale...

Ali Jita ya koma jam’iyar APC daga NNPP

Mataimakin shugaban majalisar dattawa dattawa, Sanata Barau Jibrin ya karɓi fitaccen mawakin Kannywood, Aliyu Isa Jita daga jam'iyar NNPP ya zuwa jam'iyar APC. Ali Jita...

An yi jana’izar mutumin da ya Æ™irÆ™iri tutar Najeriya

Iyalan marigayi, Pa Taiwo Akinkumi mutumin da ya ƙirƙiro tutar Najeriya sun yi bikin binne shi bayan da gwamnatin tarayya ta gaza cika alƙawarin...

‘Za a Æ™ara wa Æ´an bautar Æ™asa na NYSC alawus’

Babban daraktan hukumar yi wa kasa hidima ta kasa (NYSC) Birgediya Janar Yushau Ahmed, ya tabbatar wa ‘yan bautar kasar cewa za a kara...