Gwamnonin PDP :Mun gamsu cewa Kotun Ƙoli Za Ta Yi Adalci A Shari’ar Zaɓukan Gwamnonin Zamfara Da Filato

Gwamnonin da aka zaɓa ƙarƙashin jam’iyar PDP sun ce sun gamsu cewa kotun ƙoli za ta “yi adalci” a shari’o’in zaɓen gwamna da suka samu rashin nasara.

Matsayar gwamnonin na ƙunshe ne cikin wata sanarwa da aka fitar ranar Alhamis a ƙarshen taron da suka gudanar a Abuja.

Gwamnonin sun ce sun tattauna kan abubuwa da dama da suke da alaƙa da su da kuma waɗanda suka damu kungiyar da suka haɗa da sake duba hukuncin kotun ɗaukaka ƙara kan wasu zaɓukan gwamna da suka haɗa da na Zamfara da Filato

“A matsayin mu na kungiya muna sake jaddada kwarin gwiwar da muke da shi kan bangaren shari’a zai yi adalci,” a cewar sanarwar mai ɗauke da sa hannun gwamnan jihar Bauchi, Bala Muhammad.

More from this stream

Recomended