Gwamnoni sun ziyarci Tinubu a Lagos

Wata tawagar kungiyar gwamnonin Najeriya sun kaiwa shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ziyara a birnin Lagos.

Da yammacin ranar Alhamis ne Tinubu ya isa Lagos daga Abuja cikin jirgin shugaban ƙasa inda ya sauka a filin jirgin saman Murtala Muhammad dake Ikeja.

Shugaban kasar ya samu tarba daga gwamnan jihar Babajide Sanwo-Olu da kuma dumbin tarin magoya baya.

A ranar Talata wani fefan bidiyo ya bayyana inda aka ga gwamnonin karkashin jagorancin gwamnan jihar Kwara, Abdulrahaman Abdulrazak suna shiga motar safa da za ta kai su gidan shugaban kasar.

Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima da kuma shugaban ma’aikatan fadar shugaban kasa, Femi Gbajabiamila na daga cikin wadanda da suke nan a lokacin ziyarar.

More News

An kama mutane biyu  masu garkuwa da mutane a jihar Kogi

Wasu É“atagari biyu da ake zargin masu garkuwa da mutane ne jami'an Æ´an sanda da haÉ—in gwiwar Æ´an bijilante suka kama a garin Ibobo-Abocho...

Jirgi mai saukar ungulu ya yi hatsari a Akwa Ibom

Wasu ma'aikatan kamfanin haƙar man fetur su 6 da kuma matuƙan jirgi su biyu su mutu a wani hatsarin jirgi mai saukar ungulu a...

Tinibu ya aikawa da majalisar dattawa sunaye 7 na  ministocin da zai naÉ—a

Shugaban ƙasa, Bola Ahmad Tinubu ya yi kira ga majalisar dattawa da ta tabbatar da sunayen mutane 7 da ya tura majalisar da zai...

Gwamnatin Abia za ta fara biyan albashi mafi maranci na naira 70,000 a watan Oktoba

Gwamnatin Jihar Abia ta sanar da cewa za ta fara biyan sabon albashi mafi karanci na naira 70,000 ga ma’aikatanta daga watan Oktoba 2024.Kwamishinan...