Gwamnatin tarayya ta ce zata jingine batun karbar harajin VAT kan man Diesel har sai bayan nan da wata shida a wani mataki na rage raɗaɗin cire tallafin man fetur.
Hakan na cikin matsayar da aka cimma tsakanin gwamnatin tarayya da yan kungiyoyin ƙwadago ta NLC da TUC da gwamnatin a taron da suka yi jiya.
Da yake magana a karshen taron ganawar da aka yi shugaban ma’aikatan fadar shugaban kasa, Femi Gbajabiamila ya ce gwamnatin da kungiyar ƙwadago sun cimma wasu matsayoyi.
Sai dai wasu masana na ganin ya kamata gwamnati ta dauki matakai na dindindin domin magance tsadar rayuwa da yan Najeriya ke fama da ita.